Skip to main content

Posts

Ganduje ya bai wa makaho aiki saboda bajintarsa

Recent posts

Trump zai kirkiro da manhajar Intanet kamar Facebook

Tsohon shugaban kasar Amurka Donal Trump zai bude shafin Intanet mai kama da Facebook da ya radawa suna Gaskiya da Gaskiya Rahoto: Comrade Musa Garba Augie. Donald Trump ya sanar da shirin kaddamar da wani sabon shafin sada zumunta. Shafin wanda zai sanya wa suna Gaskiya da Gaskiya, zai kasance karkashin gudanarwar wata kungiyar da ke kula da harkokin kimiyya da fasaha a tafiyarsa ta siyasa. Tsohon shugaban ya ce zai kirkikiri kamfanin ne da fatan jama'a za su yi abun da ya kira zaluncin manyan kamfanonin fasaha, irinsu Facebook da Twitter bara'a. Ana sa ran Shafin Gaskiya da Gaskiya na Mista Trump, zai fara aiki a watan Nuwamba tare da wasu kayyadaddun mutane da za su fara amfani da shi a matsayin gwaji, kafin daga baya ya zama na kowa da kowa. A baya dai shafukan Facebook da na Twitter suka rufe shafin tsohon shugaban Amurkan saboda harin da magoya bayansa suka kai wa majalisar kasar.

Najeriya ta ce ita mamba ce ta Majalisar Ɗinkin Duniya wadda take da dokoki na kare duk wani mutum da ba shi da fasfo na wata ƙasa,

Najeriya ta ce ita mamba ce ta Majalisar Ɗinkin Duniya wadda take da dokoki na kare duk wani mutum da ba shi da fasfo na wata ƙasa, wanda a kan haka ta ƙi amsa buƙatar shugaban Turkiyya ta korar wasu ƴan ƙasarsa. Rahoto: Comrade Musa Garba Augie. Fadar Shugaban Najeriya ta yi bayani kan dalilan da suka sa gwamnatin kasar ta ƙi amincewa da bukatar shugaban Turkiyya Racib Tayyeb Erdogan na ba shi hadin kai wajen daukar mataki kan magoya bayan Fathullah Gullen da ƙadarorinsa da ke Najeriya. Shugaba Recep Tayyip Erdoğan na Turkiyya ya ce wadanda suka shirya yi masa juyin mulki a 2016 suna nan har yanzu a Najeriya suna gudanar da harkokinsu inda ya nemi hadin kan Najeriya wajen murkushe su. Erdogan ya bayyana hakan ne a ranar Laraba yayin ziyararsa ta kwana biyu a Najeriya, inda suka tattauna kan batutuwa da yawa na alaƙa tsakaninsa da Shugaba Buhari. Sai dai ba wannan ne karo na farko da Turkiyya take neman wannan buƙatar ba, ta sha neman hakan ta wajen jakadanta da ke Najeriya

Gwamnatin Kaduna ta ce an kashe mutum 343 cikin wata uku a jihar

Daga: Comrade Musa Garba Augie. Gwamnatin Jihar Kaduna ta tabbatar da mutuwar mutum 343 sakamakon ayyukan 'yan fashin daji da sauran tashe-tashen hankali cikin wata uku. Cikin wani rahoto da ya fitar ranar Laraba, Kwamashinan Tsaro da Harkokin Cikin Gida na Kaduna Samuel Aruwan ya bayyana cewa 'yan bindigar da ake zaton 'yan fashin daji ne sun sace mutum 830 a watannin. Rahoton ya duba rikice-rikicen da suka faru ne daga 1 ga watan Yuli zuwa 30 ga Satumban 2021. Sai dai rahoton ya nuna cewa adadin waɗanda aka sace a wata ukun ya ƙaru a kan na watannin Afrilu zuwa Yuni, inda aka sace 774 kuma aka kashe 222. •Na cire ɗana daga makarantar gwamnati saboda 'yan fashi na ƙoƙarin sace shi - El-Rufai •'Yan bindiga sun kai hari Makarantar Sojoji ta NDA •Abin da ya sa El-Rufai ba ya goyon bayan yin sulhu da ƴan bindiga •A gefe guda kuma, Mista Aruwan ya ce jami'an tsaro sun kashe jumillar 'yan fashi 69 a wurare daba-daban na jihar tare da tarwatsa sansanon

Kotu ta umarci kakakin majalisar Kano da wasu mutane 5 su gurfana a gabanta

Wata babbar kotun tarayya da ke Kano a ranar Laraba, ta umarci kakakin majalisar jihar Kano da wasu mutane biyar su gurfana a gabanta.  Wannan umurnin ya biyo bayan wata takarda da aka shigar ta tsohon Shugaban Korafe-korafen Jama'a da Yaki da Cin Hanci da Rashawa na Jihar Kano, Muhyi Rimin-Gado wanda gwamnatin Kano ta dakatar a watannin baya.  Sauran wadanda ake kara sun hada da Kwamishinan Shari'a na Kano, Babban Akantan jihar Kano, Kwamishinan 'yan sanda na Kano da Sufeto Janar na' yan sanda.  Mai shari’a Jane Inyang, wacce ta ba da umarnin, ta nemi su kawo dalili cikin kwanaki biyar da zai sa kotu ba za tayi abinda wanda ya gabatar da ƙara ya nema ba.  Inyang ta bada umarnin a sanar da wadanda ake kara a cikin kwanaki biyar sannan ta dage karar zuwa ranar 3 ga Nuwamba, don cigaba da sauraron karar.  Tun da farko, mai gabatar da kara Rimin-Gado a cikin karar ta bakin lauyansa Barista Muhammad Dan’azumi ya gabatar, ya nemi a hana mutane shida da ake kara b

A karon farko an bi umarnin IPOB na zama a gida a Abia Ikpeazu

Manyan tituna sun zama wayam, sannan shaguna da ma'aikatun gwamnati sun kasance a rufe a fadin Umuahia babban birnin jihar Abia da ke kudancin Najeriya, sakamakon kullen da kungiyar 'yan awaren Biafra ta IPOB ta saka. Ko a baya IPOB ta saka irin wannan doka ta zama a gida, da ya hada da rufe makarantu da kasuwanni amma ba ta yi tasiri ba. A Litinin din da ta gabata mazauna birnin Umuahia sun ce mambobin IPOB sun rika yawo da bindigogi kan tituna, suna hantarar mutane su shige gidajensu. To sai dai mazauna babban birnin jahar ta Abia sun sami kansu cikin tsaka mai wuya, bayan da gwamnatin jahar ta yi gargaɗin cewa duk ma'aikacin da bai fito aiki ba zai fuskanci hukunci. To amma bayanai daga jaridar Daily Trust sun nuna cewa kashi 80 basu fita aiki ba a yau Litinin.

Wasu jigajigai a jam'iyyar PDP sun sauya sheka zuwa APC a jihar Yobe

Mataimakin shugaban PDP da wasu manyan shugabanni sun sauya sheƙa zuwa Jam'iyyar APC a jihar Yobe dake Arewa maso gabashin Nigeria. Mataimakin shugaban PDP reshen jihar Yobe, tare da wasu manyan jiga-jigai sun koma jam'iyyar APC mai mulki A cewar waɗanda suka sauya shekan, ba bu wani dalili da zai sa su cigaba da zama cikin PDP, saboda shugaban ƙasa na bukatar goyon baya Gwamna Mai Mala Buni, na jihar Yobe, ya tabbatar musu da cewa ba za'a nuna musu banbanci ba. Wasu daga cikin shugabannin jam'iyyar hammaya PDP reshen jihar Yobe, tare da mambobi sun sauya sheƙa zuwa jam'iyyar APC mai mulki. Vanguard ta rahoto cewa daga cikin waɗanda suka koma APC har da, mataimakin shugaban PDP na jiha, Alhaji Usman Amale, da mataimakin sakatare, Malam Ahmadu Biriri. Jaridar Illela Daily Post ta ruwaito cewa gwamnan Yobe, Mai Mala Buni, shine ya karbi masu sauya shekan ranar Talata a Damaturu. Gwamna Mai Mala Buni, wanda shine shugaban kwamitin rikon kwarya na APC ta ƙas