Skip to main content

Kotu ta umarci kakakin majalisar Kano da wasu mutane 5 su gurfana a gabanta


Wata babbar kotun tarayya da ke Kano a ranar Laraba, ta umarci kakakin majalisar jihar Kano da wasu mutane biyar su gurfana a gabanta. 

Wannan umurnin ya biyo bayan wata takarda da aka shigar ta tsohon Shugaban Korafe-korafen Jama'a da Yaki da Cin Hanci da Rashawa na Jihar Kano, Muhyi Rimin-Gado wanda gwamnatin Kano ta dakatar a watannin baya. 

Sauran wadanda ake kara sun hada da Kwamishinan Shari'a na Kano, Babban Akantan jihar Kano, Kwamishinan 'yan sanda na Kano da Sufeto Janar na' yan sanda. 

Mai shari’a Jane Inyang, wacce ta ba da umarnin, ta nemi su kawo dalili cikin kwanaki biyar da zai sa kotu ba za tayi abinda wanda ya gabatar da ƙara ya nema ba. 

Inyang ta bada umarnin a sanar da wadanda ake kara a cikin kwanaki biyar sannan ta dage karar zuwa ranar 3 ga Nuwamba, don cigaba da sauraron karar. 

Tun da farko, mai gabatar da kara Rimin-Gado a cikin karar ta bakin lauyansa Barista Muhammad Dan’azumi ya gabatar, ya nemi a hana mutane shida da ake kara bincike da sake tsare shi.

Barista Dan’azumi ya kuma roki kotun da ta yi la’akari da abinda mai gabatar da ƙara ya nema, ya kara da cewa wadanda ake kara sun saɓa wa umarnin da babbar kotun Kano ta bayar a baya. 

Idan ba a manta ba, wata babbar kotun Kano karkashin jagorancin Mai Shari’a Sanusi Ado-Ma’aji, a ranar 23 ga Yuli, ta hana Majalisar Dokokin Jihar Kano, Akanta Janar na Jihar Kano da wasu mutum biyu daga ci gaba da binciken Rimin-Gado. 

Kamfanin dillancin labarai na NAN ya rawaito cewa a ranar 5 ga watan Yuli majalisar dokokin Kano ta dakatar da Muhuyi Magaji saboda kin amincewa da akawun da aka kawo masa daga ofishin Babban Akanta na jihar.

Comments

Popular posts from this blog

EFCC ta ƙaddamar da sabon salon yaƙi da rashawa a Najeriya

Shugaban EFCC Abdurrashid  Bawa Shugaban EFCC Abdulrasheed Bawa ya ce hukumar za ta fifita daƙile aikata laifuka kafin a aikata su Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta EFCC a Najeriya ta ce ta ɓullo da wani sabon salon daƙile ayyukan rashawa, inda za ta fi mayar da hankali kan rigakafin daƙile laifin kafin a aikata shi. A cewar Shugaban EFCC Abdulrasheed Bawa, daga yanzu hukumar za ta fi mayar da hankali wajen haɗa kai da abokan hulɗarta musamman na ƙasashen waje domin yaƙi da ayyukan rashawa. Da yake magana yayin taron ƙaddamar da sabon tsarin aikin a Abuja, Abdulrasheed Bawa ya ce sabon tsarin na 2021 zuwa 2025 an ciro shi ne daga kundin muradai na EFCC na shekarar 2013 zuwa 2018. "Sabon salon ya fi fifita rigakafi (hana faruwar laifi) a matsayin hanya mafi sauƙin daƙile rashawa fiye da yin hukunci," a cewarsa kamar yadda mujallar EFCC ta mako-mako ta ruwaito. Ya ƙara da cewa sabon tsarin zai fifita tattara bayanan sirri da gurfanar da masu laifi a gaban kotu...

Ganduje ya bai wa makaho aiki saboda bajintarsa

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya bai wa Ɗahuru Abdulhamid Idris wanda makaho ne, aikin koyarwa a gwamnatin jihar. Bayanin haka na ƙunshe ne cikin sanarwar da Sakataren Labarai na gwamnatin jihar, Abba Anwar ya fitar a ranar Lahadi. Kafin wannan lokaci, Ɗahuru ya kasance yana aikin koyarwa na sa-kai ba tare da ana biyansa wani albashi ba. Sanarwar ta ce bayan da Kwamishinan Ilimi na Jihar Kano, Muhammadu Sanusi Kiru, ya jagoranci Ɗahuru zuwa gaban Ganduje ne, a nan Ganduje ya bada umarnin a ɗauke shi aiki sannan a tura shi Makarantar Nakasassu da ke Tudun Maliki don ya ci gaba koyarwa. Yayin ganawar tasu, Ganduje ya yaba wa ƙoƙarin Ɗahuru musamman ma ganin yadda bai bari lalurar makanta ta hana shi bada tasa gudunmawa ga cigaban fannin ilimin jihar ba. Bisa wannan dalili ne Gwamna Ganduje ya ce, “Lallai ka taki matakin da ya dace a rayuwarka. Gwamnatin jihar Kano ta ba ka aikin koyarwa. Kuma na umarci Kwamishinan Ilimi da a tura ka zu...

PDP za ta 'Kwace mulki daga hannun APC a zaben 2023 - Inji Atiku Abubakar

Alh. Atiku Abubakar Tsohon mataimakin shugaban kasar Najeriya, Alhaji Atiku Abubakar ya bayyana kwarin gwiwar cewa jam'iyyar PDP, Mai adawa, za ta karbi mulki daga hannun jam'iyyar APC, mai mulki, a zaben shekarar 2023. Atku Abubakar ya bayyana hakan ne yayin da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan ya kada kuri'arsa a dandalin Mahmud Ribadu, Yola, wurin za'ben shugabannin  jam'iyyar PDP na jiha. Ya yi kira ga 'yan siyasa da su mutunta dokokin jam'iyya, na za'be, da Kuma na kundin tsarin mulkin kasar wajen zaben shugabannin jam'iyya, yana mai cewa dimokradiyya na iya 'dorewa ne a cikin yanayi na 'yanci da adalci