Wata babbar kotun tarayya da ke Kano a ranar Laraba, ta umarci kakakin majalisar jihar Kano da wasu mutane biyar su gurfana a gabanta.
Wannan umurnin ya biyo bayan wata takarda da aka shigar ta tsohon Shugaban Korafe-korafen Jama'a da Yaki da Cin Hanci da Rashawa na Jihar Kano, Muhyi Rimin-Gado wanda gwamnatin Kano ta dakatar a watannin baya.
Sauran wadanda ake kara sun hada da Kwamishinan Shari'a na Kano, Babban Akantan jihar Kano, Kwamishinan 'yan sanda na Kano da Sufeto Janar na' yan sanda.
Mai shari’a Jane Inyang, wacce ta ba da umarnin, ta nemi su kawo dalili cikin kwanaki biyar da zai sa kotu ba za tayi abinda wanda ya gabatar da ƙara ya nema ba.
Inyang ta bada umarnin a sanar da wadanda ake kara a cikin kwanaki biyar sannan ta dage karar zuwa ranar 3 ga Nuwamba, don cigaba da sauraron karar.
Tun da farko, mai gabatar da kara Rimin-Gado a cikin karar ta bakin lauyansa Barista Muhammad Dan’azumi ya gabatar, ya nemi a hana mutane shida da ake kara bincike da sake tsare shi.
Barista Dan’azumi ya kuma roki kotun da ta yi la’akari da abinda mai gabatar da ƙara ya nema, ya kara da cewa wadanda ake kara sun saɓa wa umarnin da babbar kotun Kano ta bayar a baya.
Idan ba a manta ba, wata babbar kotun Kano karkashin jagorancin Mai Shari’a Sanusi Ado-Ma’aji, a ranar 23 ga Yuli, ta hana Majalisar Dokokin Jihar Kano, Akanta Janar na Jihar Kano da wasu mutum biyu daga ci gaba da binciken Rimin-Gado.
Kamfanin dillancin labarai na NAN ya rawaito cewa a ranar 5 ga watan Yuli majalisar dokokin Kano ta dakatar da Muhuyi Magaji saboda kin amincewa da akawun da aka kawo masa daga ofishin Babban Akanta na jihar.
Comments
Post a Comment