Skip to main content

Najeriya ta ce ita mamba ce ta Majalisar Ɗinkin Duniya wadda take da dokoki na kare duk wani mutum da ba shi da fasfo na wata ƙasa,

Najeriya ta ce ita mamba ce ta Majalisar Ɗinkin Duniya wadda take da dokoki na kare duk wani mutum da ba shi da fasfo na wata ƙasa, wanda a kan haka ta ƙi amsa buƙatar shugaban Turkiyya ta korar wasu ƴan ƙasarsa.
Rahoto: Comrade Musa Garba Augie.

Fadar Shugaban Najeriya ta yi bayani kan dalilan da suka sa gwamnatin kasar ta ƙi amincewa da bukatar shugaban Turkiyya Racib Tayyeb Erdogan na ba shi hadin kai wajen daukar mataki kan magoya bayan Fathullah Gullen da ƙadarorinsa da ke Najeriya.

Shugaba Recep Tayyip Erdoğan na Turkiyya ya ce wadanda suka shirya yi masa juyin mulki a 2016 suna nan har yanzu a Najeriya suna gudanar da harkokinsu inda ya nemi hadin kan Najeriya wajen murkushe su.

Erdogan ya bayyana hakan ne a ranar Laraba yayin ziyararsa ta kwana biyu a Najeriya, inda suka tattauna kan batutuwa da yawa na alaƙa tsakaninsa da Shugaba Buhari.

Sai dai ba wannan ne karo na farko da Turkiyya take neman wannan buƙatar ba, ta sha neman hakan ta wajen jakadanta da ke Najeriya, amma gwamnati na yin biris da buƙatar.

Mataimaki na musamman ga shugaban Najeriya kan harkokin yada labarai, Mallam Garba Shehu ya nuna cewa matsayin shugaban kasar na ƙin amsa bukatar shugaban Turkiyya ta rufe makarantu da asibitoci da sauran harkoki na wadanda kasar ke zargi da yunkurin kifar da gwamnati bai sauya ba kamar a baya.

Ita dai gwamnatin Erdogan tana zargin mabiya kungiyar fitaccen malamin addinin Musuluncin nan da ke zaune a Amurka Fethullah Gulen da yunkurin kifar da gwamnatinsa, kuma tana daukar makarantu da asibitocin ƴan Turkiyya da ke Najeriya a matsayin na magoya bayan malamin.

Shi dai Fethullah Gulen wanda tsohon makusancin Erdogan ne, ya musanta wannan zargi na yunƙurin, wanda bai yi nasara ba, wanda kuma ya kai ga hallaka farar hula sama da 250, tare da kama dubban mutane da gwamnatin ta zarga da hannu a ciki.

Yawancin wadanda aka zarga da yunkurin jami'an tsaron fadar shugaban kasar ne.

Tun bayan yunkurin Shugaba Erdogan na harin magoy bayan malamin, inda da yawa daga cikin ƴan kasar da ke aiki da gwamnati da ma sojoji suka rasa ayyukansu bisa zargin goyon baya da kungiyar malamin.

A hirarsa da BBC, Garba Shehu ya ce ko a ziyarar baya wadda shugaban na Turkiyya ya zo Najeriya a ranar 1 ga watan Maris na 2016, Erdogan ya gabatar wa da Buhari wannan bukata ta rufe harkokin ƴan kasar tasa da yake zargi da neman hambarar da gwamnatinsa, bisa alkawarin cewa su za su kawo wasu makarantun da asibitoci su maye gurbin wadannan.

Kakakin na Buhari ya ce har a yanzu da shugaban na Turkiyya ya kara gabatar da wannan bukata, amsar da Shugaba Buharin ya ba shi kamar a wancan lokacin ba ta sauya.

"To ai wannan magana da ma ba sabuwa ba ce, ko wancan karo da ya zo, a hakika ya nemi cewa a rufe su makarantu, asibitoci da sauransu su za su kawo sababbi a kafa.

"Amsa da Shugaba Buhari ya bayar a wancan lokaci shi ne, Najeriya ƙawa ce ga Turkiyya muna da dangantaka kyakkyawa tsakaninmu.

"In ma ban da haka babu wata kasa ta duniya da za mu yarda mu nan Najeriya a yi amfani da kasarmu a kafa sansani don cin zarafi ko don a kawo tashin hankali a wata kasa."

"Saboda haka wannan ziyarar da aka kawo wa Shugaba Muhammadu Buhari ya jaddada wannan matsayi nasa bai canja ba," in ji Garba Shehu.

Dangane da cewa ko za a dauki matakin rufe makarantun da asibitocin sai kakakin ya ce, "A'a cewa mu a matsayinmu na mambobi na Majalisar Dinkin Duniya ai akwai ƙa'idoji iri daban-daban da MDD ta ajiye don kare hakki ƴan kasa wadanda ba su da fasfo a ko ina suke a duniya.

"Wannan Majalisar Dinkin Duniya ke musu gata a dauka cewa kasarsu Majalisar Dinkin Duniya ce."

Mataimakin na musamman ga Shugaba Buhari ya kara da bayanin cewa maganar da shugaban na Turkiyya ya yi a dunkule take, "mu ma tamu a dunkule take saboda haka ina ganin akwai kyakkyawar fahimtar juna."

Akwai dai asibitoci da makarantun furamare da na sakandire har ma da jami'a na ƴan Turkiyya a wasu jihohin Najeriya, wadanda Erdogan ke zargin dukkaninsu suna da alaka da magoy bayan Sheikh Gulen.

Abubuwan da ziyarar ta Erdogan ta cimma a Najeriya
A yayin ziyarar ta kwana biyu ta shugaban na Turkiya wanda ya sauka a Abuja ranar Talata 19 ga watan Oktoba 2021, tare da matarsa, Emine Erdoğan.

Kazalika ya zo da ministan harkokin waje, Mevlüt Çavuşoğlu, da ta Muhalli, Fatma Güldemet Sarı, da na tattalin arziki Mustafa Elitaş, da na makamashi, Berat Albayrak, da na tsaro İsmet Yılmaz da kuma manyan 'yan kasuwar kasar.

Kasashen biyu sun kulla yarjeniyoyi kusan guda takwas a tsakaninsu.

Sun hada da takaita karbar haraji a tsakanin kamfanonin kasashen biyu da harkar ma'adanai da batutuwan tsaro da makamashi na wutar lantarki da gas da tallafa wa matasa da kuma harkokin siyasar duniya.

Comments

Popular posts from this blog

Buhari ya fusata da kisar gillar da aka yi wa masu cin kasuwa a garin Goronyo dake gabashin jihar Sokoto.

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yi matukar fusata da kisan gillar da aka yi wa masu cin Kasuwa a Goronyo, Jihar Sokoto inda ya aika wa ƴan bindiga sakon ‘Ta su ta kare’ ranar Litinin. Kakakin fadar shugaban ƙasa, Garba Shehu a wata takarda daga fadar shugaba Buhari ranar Litinin ya bayyana cewa shugaban Buhari ya fusata matuka da kisan da aka yi wa ƴan kasuwa da basu ji ba basu gani ba a kasuwar goronyo. Buhari ya ce wannan karon ƴan bindigan sun kai gwamnati maƙura kuma sun siya da kuɗin su domin sai sun gwammace kiɗa da karatu nan ba da daɗewa ba. ” Ko a yanzu ba su ji da daɗi daga dakarun Najeriya ta sama da kasa ba. Hakan yasa suke bin mutanen da basu ji ba basu gani suna kashe su. Wannan abu ya kai mu makura yanzu kuma lallai su kwana da shirin ta su ta kare. Harin Goronyo A kasuwar Goronyo jihar Sokoto dake ci mako-mako ne ‘yan bindiga suka buda wa mutane wuta inda suka kashe mutum sama da 30 sannan da dama sun ji rauni. Wannan hari ya auku ne kwanaki 12 da wasu ‘ya

Gwamnatin Kaduna ta ce an kashe mutum 343 cikin wata uku a jihar

Daga: Comrade Musa Garba Augie. Gwamnatin Jihar Kaduna ta tabbatar da mutuwar mutum 343 sakamakon ayyukan 'yan fashin daji da sauran tashe-tashen hankali cikin wata uku. Cikin wani rahoto da ya fitar ranar Laraba, Kwamashinan Tsaro da Harkokin Cikin Gida na Kaduna Samuel Aruwan ya bayyana cewa 'yan bindigar da ake zaton 'yan fashin daji ne sun sace mutum 830 a watannin. Rahoton ya duba rikice-rikicen da suka faru ne daga 1 ga watan Yuli zuwa 30 ga Satumban 2021. Sai dai rahoton ya nuna cewa adadin waɗanda aka sace a wata ukun ya ƙaru a kan na watannin Afrilu zuwa Yuni, inda aka sace 774 kuma aka kashe 222. •Na cire ɗana daga makarantar gwamnati saboda 'yan fashi na ƙoƙarin sace shi - El-Rufai •'Yan bindiga sun kai hari Makarantar Sojoji ta NDA •Abin da ya sa El-Rufai ba ya goyon bayan yin sulhu da ƴan bindiga •A gefe guda kuma, Mista Aruwan ya ce jami'an tsaro sun kashe jumillar 'yan fashi 69 a wurare daba-daban na jihar tare da tarwatsa sansanon

Sokoto: 'Ƴan bindiga sun kashe mutum 49 a kasuwar Goronyo'

Tambuwal Rahotanni daga jihar Sokoto a arewa maso yammacin Najeriya na cewa ƴan bidnga sun kashe aƙalla mutum 49 a wata kasuwa a garin Goronyo na jihar. Wasu ganau sun tabbatar wa da BBC labarin inda suka ce lamarin ya faru ne a ranar Lahadi da yamma, yayin da mutanen ke cin babbar kasuwar Goronyon. Mutanen waɗanda suka buƙaci a sakaya sunayensu saboda tsaro sun ce ƴan bindigar sun afka wa kasuwar ne a yayin da ta cika makil da masu hada-hada daga sassan jihar da ma wasu yankunan. "Ƴan fashin sun zo ne da misalin ƙarfe 4.30 zuwa biyar na yamma suka zagaye kasuwar suka buɗe wuta ta kowane ɓangare," in ji ganau ɗin. Majiyarmu ta yi ƙoƙarin jin ta bakin rund8nar ƴan sanda jihar, amma ba mu samu mai magana da yawun ƴan sanda ba a kiran waya da aka yi ta yi masa. Ya ƙara da cewa "Mutane duk suka ruɗe wasu sun kwakkwanta a ƙasa don gudun harbin ya same su, yayin da wasu suka gudu amma masu tsautsayi sun rasa rayukansu." Ganau ɗin sun ce an ƙidaya gawa 49 yayin