Skip to main content

Najeriya ta ce ita mamba ce ta Majalisar Ɗinkin Duniya wadda take da dokoki na kare duk wani mutum da ba shi da fasfo na wata ƙasa,

Najeriya ta ce ita mamba ce ta Majalisar Ɗinkin Duniya wadda take da dokoki na kare duk wani mutum da ba shi da fasfo na wata ƙasa, wanda a kan haka ta ƙi amsa buƙatar shugaban Turkiyya ta korar wasu ƴan ƙasarsa.
Rahoto: Comrade Musa Garba Augie.

Fadar Shugaban Najeriya ta yi bayani kan dalilan da suka sa gwamnatin kasar ta ƙi amincewa da bukatar shugaban Turkiyya Racib Tayyeb Erdogan na ba shi hadin kai wajen daukar mataki kan magoya bayan Fathullah Gullen da ƙadarorinsa da ke Najeriya.

Shugaba Recep Tayyip Erdoğan na Turkiyya ya ce wadanda suka shirya yi masa juyin mulki a 2016 suna nan har yanzu a Najeriya suna gudanar da harkokinsu inda ya nemi hadin kan Najeriya wajen murkushe su.

Erdogan ya bayyana hakan ne a ranar Laraba yayin ziyararsa ta kwana biyu a Najeriya, inda suka tattauna kan batutuwa da yawa na alaƙa tsakaninsa da Shugaba Buhari.

Sai dai ba wannan ne karo na farko da Turkiyya take neman wannan buƙatar ba, ta sha neman hakan ta wajen jakadanta da ke Najeriya, amma gwamnati na yin biris da buƙatar.

Mataimaki na musamman ga shugaban Najeriya kan harkokin yada labarai, Mallam Garba Shehu ya nuna cewa matsayin shugaban kasar na ƙin amsa bukatar shugaban Turkiyya ta rufe makarantu da asibitoci da sauran harkoki na wadanda kasar ke zargi da yunkurin kifar da gwamnati bai sauya ba kamar a baya.

Ita dai gwamnatin Erdogan tana zargin mabiya kungiyar fitaccen malamin addinin Musuluncin nan da ke zaune a Amurka Fethullah Gulen da yunkurin kifar da gwamnatinsa, kuma tana daukar makarantu da asibitocin ƴan Turkiyya da ke Najeriya a matsayin na magoya bayan malamin.

Shi dai Fethullah Gulen wanda tsohon makusancin Erdogan ne, ya musanta wannan zargi na yunƙurin, wanda bai yi nasara ba, wanda kuma ya kai ga hallaka farar hula sama da 250, tare da kama dubban mutane da gwamnatin ta zarga da hannu a ciki.

Yawancin wadanda aka zarga da yunkurin jami'an tsaron fadar shugaban kasar ne.

Tun bayan yunkurin Shugaba Erdogan na harin magoy bayan malamin, inda da yawa daga cikin ƴan kasar da ke aiki da gwamnati da ma sojoji suka rasa ayyukansu bisa zargin goyon baya da kungiyar malamin.

A hirarsa da BBC, Garba Shehu ya ce ko a ziyarar baya wadda shugaban na Turkiyya ya zo Najeriya a ranar 1 ga watan Maris na 2016, Erdogan ya gabatar wa da Buhari wannan bukata ta rufe harkokin ƴan kasar tasa da yake zargi da neman hambarar da gwamnatinsa, bisa alkawarin cewa su za su kawo wasu makarantun da asibitoci su maye gurbin wadannan.

Kakakin na Buhari ya ce har a yanzu da shugaban na Turkiyya ya kara gabatar da wannan bukata, amsar da Shugaba Buharin ya ba shi kamar a wancan lokacin ba ta sauya.

"To ai wannan magana da ma ba sabuwa ba ce, ko wancan karo da ya zo, a hakika ya nemi cewa a rufe su makarantu, asibitoci da sauransu su za su kawo sababbi a kafa.

"Amsa da Shugaba Buhari ya bayar a wancan lokaci shi ne, Najeriya ƙawa ce ga Turkiyya muna da dangantaka kyakkyawa tsakaninmu.

"In ma ban da haka babu wata kasa ta duniya da za mu yarda mu nan Najeriya a yi amfani da kasarmu a kafa sansani don cin zarafi ko don a kawo tashin hankali a wata kasa."

"Saboda haka wannan ziyarar da aka kawo wa Shugaba Muhammadu Buhari ya jaddada wannan matsayi nasa bai canja ba," in ji Garba Shehu.

Dangane da cewa ko za a dauki matakin rufe makarantun da asibitocin sai kakakin ya ce, "A'a cewa mu a matsayinmu na mambobi na Majalisar Dinkin Duniya ai akwai ƙa'idoji iri daban-daban da MDD ta ajiye don kare hakki ƴan kasa wadanda ba su da fasfo a ko ina suke a duniya.

"Wannan Majalisar Dinkin Duniya ke musu gata a dauka cewa kasarsu Majalisar Dinkin Duniya ce."

Mataimakin na musamman ga Shugaba Buhari ya kara da bayanin cewa maganar da shugaban na Turkiyya ya yi a dunkule take, "mu ma tamu a dunkule take saboda haka ina ganin akwai kyakkyawar fahimtar juna."

Akwai dai asibitoci da makarantun furamare da na sakandire har ma da jami'a na ƴan Turkiyya a wasu jihohin Najeriya, wadanda Erdogan ke zargin dukkaninsu suna da alaka da magoy bayan Sheikh Gulen.

Abubuwan da ziyarar ta Erdogan ta cimma a Najeriya
A yayin ziyarar ta kwana biyu ta shugaban na Turkiya wanda ya sauka a Abuja ranar Talata 19 ga watan Oktoba 2021, tare da matarsa, Emine Erdoğan.

Kazalika ya zo da ministan harkokin waje, Mevlüt Çavuşoğlu, da ta Muhalli, Fatma Güldemet Sarı, da na tattalin arziki Mustafa Elitaş, da na makamashi, Berat Albayrak, da na tsaro İsmet Yılmaz da kuma manyan 'yan kasuwar kasar.

Kasashen biyu sun kulla yarjeniyoyi kusan guda takwas a tsakaninsu.

Sun hada da takaita karbar haraji a tsakanin kamfanonin kasashen biyu da harkar ma'adanai da batutuwan tsaro da makamashi na wutar lantarki da gas da tallafa wa matasa da kuma harkokin siyasar duniya.

Comments

Popular posts from this blog

Kamfanin Facebook Zai Canza Sunan Sa.

LABARU DA DUMI-DUMIN SU! Shahararren dandalin sada zumunta na Facebook Inc yana shirin sake sunan kansa da sabon suna a mako mai zuwa, shafin yanar gizo na fasahar Amurka Verge ya ruwaito a ranar Talata, inda ya ambaci wata majiya da ke da masaniya kai tsaye kan lamarin.  Babban Jami'i kuma Shugaban Facebook Mark Zuckerberg yana shirin yin magana game da canjin sunan a taron haɗin gwiwa na kamfani na shekara -shekara a ranar 28 ga Oktoba, amma ana iya bayyana shi da wuri, inji rahoton Verge. Labarin na zuwa ne a daidai lokacin da kamfanin ke fuskantar karuwar sanya ido daga gwamnati a Amurka kan harkokin kasuwancinsa.  Sake canza sunan zai sanya aikace -aikacen kafofin watsa labarun Facebook a matsayin ɗayan samfura da yawa a ƙarƙashin kamfanin, wanda kuma zai kula da sauran manhajojin sa kamar Instagram, WhatsApp, Oculus da sauran su, in ji rahoton Verge.  Ba sabon abu bane a Silicon Valley don kamfanoni sun canza sunayensu yayin da suke neman fadada ayyukan ...

Musulmai Sun Yi Martani Ga Gumi Bayan Sukar Da Yayi Akan Maulud

Musulman Najeriya sun mamaye shafin Facebook na Dr. Ahmad Gumi. shahararren mai fafutukar kare hakkin ‘yan fashin daji bayan yayi suka ga maulidi a shafin a daidai lokacin da musulman suke  tunawa da ranar haihuwar Annabi Muhammad SAWA.  A kowace shekara a cikin watan Rabi’ul Awwal, Musulmin duniya suna tunawa da ranar haihuwar Annabi Muhammad ta hanyar karanta Alƙur’ani mai girma, ƙasidun yabo ya Annabi da karanta tarihin rayuwar sa. Shafin Dr. Gumi na Facebook ya samu sharhi sama da 600 har zuwa lokacin nan a tare da cewa suka yayi akan maulidin, amma da yawan su suna rubuta "Happy Maulud,"  duk da sun karanta sukar da yayi.   Karantarwar Dr Gumi tana fuskantar tsaiko da rashin tasiri akan mutane bayan ya karkatar da hankalin sa daga taimakon waɗanda rikicin yan fashin daji ya rutsa da su a arewa maso yammacin Najeriya zuwa neman haƙƙin masu aikata laifin.

Sanata Uba Sani ya Gina Makarantun ilimin fasahar Sadarwar zamani a mazabar sa

  A jihar kaduna A kokarin sa na Samar da ingantaccen ilimin zamani ga matasan ‘yan mazabarsa Sanata Uba Sani ya gina tare da samar da kayan aikin cibiyoyin Fasahar Sadarwar Zamani ICT a wasu kananan hukumomi cikin bakwai da Sanatan ke wakiltar a majalisar dattijan Nageriya An Samar da cibiyoyin ne a Makarantun da Suka ha’da da… 1. Maimuna Guarzo sakandirin gwamnatin dake Tudun Wada, a Kaduna ta Kudu, 2. Makarantar sakandaren gwamnati, Kawo, Kaduna ta Arewa da kuma 3. Makarantar sakandaren gwamnati, Turonku, karamar hukumar Igabi. (Ana Kan aiki) Samar da wannan makaratun zai ba wa malamai da ɗaliban Samun damar zama masu ilimin kwamfuta domin shiga jerin sahun sauran mutanen zamanin masu ilimin fasahar Zamani a duk matakan duniya. A Cikin ko wacce Makaranta an Samar da na’urori masu kwakwalwa (Computer) har guda ‘dari biyar 500, Jimulla dubu da ‘dari biyar 1,500. Ana sa ran Sanatan zai Samar da irin wannan makaratun a duk fa’din kananan hukumomin da yake wakilta a jihar kaduna. Anf...