Tabbas Zan Koma Jam,iyar APC Idan Har Akamin Alkawarin Kujerar Mataimakin Shugaban Kasa Azaben 2023, Cewar Kwankwaso.
Wato jama,a yanzu haka majiyar mu ta labarta mana cewa tsohon gwamnan jihar kano sanata rabi,u musa kwankwaso yama jam,iyar APC albishir da cewa idan har jam,iyar tamai alkawarin mataimakin shugaban kasa 2023 tare da masa alkawarin barin tafiyar kwankwasiya a cikin Nijeriya babu shekka zai koma jam,iyar ta APC.
Kamar yadda muka samu labarin cewa sabbin rahotanni sun fito game da shirin tsohon gwamnan Kano, Kwankwaso na komawa APC
Wasu majiyoyi masu ƙarfi sun bayyana cewa Kwankwaso ya kafa wa wakilan APC wasu sharuɗɗa kafin ya koma jam'iyyar ta APC
Kamar yadda wata majiya ta sheda mana cewa tun bayan kammala wa'adin mulkin Kwankwaso da Ganduje a 2015, har yanzu Ganduje da Kwankwaso wanda suka kasance abokan juna basa shiri amma ana kyautata zatan zasu shirya gabanin babban zaben 2023
Rahotanni sun bayyana wasu dalilai da yasa har zuwa yanzun tsohon gwamnan Kano, Rabi'u Musa Kwankwaso, bai koma APC ba didda bukatar da yake da ita a siyasan ce.
Wata majiya mai ƙarfi ta shaidawa Leadership cewa Kwankwaso na fatan tsira da mutuncinsa kuma ya kafa wa APC wasu sharuɗɗa na shiga jam'iyyar.
Kasancewar ana ta cece-kuce kuma shugabannin Arewa na ganin ya kamata a baiwa kudu takarar shugaban ƙasa a 2023, Kwankwaso ya kafawa APC sharaɗin cewa za'a ba shi kujerar mataimaki a 2023 idan har ana so yakuma jam,iyar ta APC.
Haka kuma Kwankwaso ya shaidawa APC cewa ba za'a yi karambanin ruguza tafiyarsa ta Kwankwasiyya ba a faɗin Nijeriya.
Bugu da kari, Kwankwaso ya bukaci a miƙa masa ragamar jagorancin APC a Kano, maimakon gwamna Ganduje, wanda ya kasance mataimakinsa a baya.
Majiyar mu ta tabbatar mana da cewa ba'a ga maciji tsakanin Kwankwaso da Ganduje tun bayan ƙarewar wa'adin mulkinsu a shekarar 2015.
Masu karatu ya kuke kallan kumawar kwankwaso jam,iyar APC.?
Comments
Post a Comment