Skip to main content

Tabbas zan iya komawa APC, Kwankwaso

Tabbas Zan Koma Jam,iyar APC Idan Har Akamin Alkawarin Kujerar Mataimakin Shugaban Kasa Azaben 2023, Cewar Kwankwaso. 

Wato jama,a yanzu haka majiyar mu ta labarta mana cewa tsohon gwamnan jihar kano sanata rabi,u musa kwankwaso yama jam,iyar APC albishir da cewa idan har jam,iyar tamai alkawarin mataimakin shugaban kasa 2023 tare da masa alkawarin barin tafiyar kwankwasiya a cikin Nijeriya babu shekka zai koma jam,iyar ta APC.

Kamar yadda muka samu labarin cewa sabbin rahotanni sun fito game da shirin tsohon gwamnan Kano, Kwankwaso na komawa APC

Wasu majiyoyi masu ƙarfi sun bayyana cewa Kwankwaso ya kafa wa wakilan APC wasu sharuɗɗa kafin ya koma jam'iyyar ta APC

Kamar yadda wata majiya ta sheda mana cewa tun bayan kammala wa'adin mulkin Kwankwaso da Ganduje a 2015, har yanzu Ganduje da Kwankwaso wanda suka kasance abokan juna basa shiri amma ana kyautata zatan zasu shirya gabanin babban zaben 2023

Rahotanni sun bayyana wasu dalilai da yasa har zuwa yanzun tsohon gwamnan Kano, Rabi'u Musa Kwankwaso, bai koma APC ba didda bukatar da yake da ita a siyasan ce. 

Wata majiya mai ƙarfi ta shaidawa Leadership cewa Kwankwaso na fatan tsira da mutuncinsa kuma ya kafa wa APC wasu sharuɗɗa na shiga jam'iyyar.

Kasancewar ana ta cece-kuce kuma shugabannin Arewa na ganin ya kamata a baiwa kudu takarar shugaban ƙasa a 2023, Kwankwaso ya kafawa APC sharaɗin cewa za'a ba shi kujerar mataimaki a 2023 idan har ana so yakuma jam,iyar ta APC.

Haka kuma Kwankwaso ya shaidawa APC cewa ba za'a yi karambanin ruguza tafiyarsa ta Kwankwasiyya ba a faɗin Nijeriya.

Bugu da kari, Kwankwaso ya bukaci a miƙa masa ragamar jagorancin APC a Kano, maimakon gwamna Ganduje, wanda ya kasance mataimakinsa a baya. 

Majiyar mu ta tabbatar mana da cewa ba'a ga maciji tsakanin Kwankwaso da Ganduje tun bayan ƙarewar wa'adin mulkinsu a shekarar 2015. 

Masu karatu ya kuke kallan kumawar kwankwaso jam,iyar APC.?

Comments

Popular posts from this blog

Kamfanin Facebook Zai Canza Sunan Sa.

LABARU DA DUMI-DUMIN SU! Shahararren dandalin sada zumunta na Facebook Inc yana shirin sake sunan kansa da sabon suna a mako mai zuwa, shafin yanar gizo na fasahar Amurka Verge ya ruwaito a ranar Talata, inda ya ambaci wata majiya da ke da masaniya kai tsaye kan lamarin.  Babban Jami'i kuma Shugaban Facebook Mark Zuckerberg yana shirin yin magana game da canjin sunan a taron haɗin gwiwa na kamfani na shekara -shekara a ranar 28 ga Oktoba, amma ana iya bayyana shi da wuri, inji rahoton Verge. Labarin na zuwa ne a daidai lokacin da kamfanin ke fuskantar karuwar sanya ido daga gwamnati a Amurka kan harkokin kasuwancinsa.  Sake canza sunan zai sanya aikace -aikacen kafofin watsa labarun Facebook a matsayin ɗayan samfura da yawa a ƙarƙashin kamfanin, wanda kuma zai kula da sauran manhajojin sa kamar Instagram, WhatsApp, Oculus da sauran su, in ji rahoton Verge.  Ba sabon abu bane a Silicon Valley don kamfanoni sun canza sunayensu yayin da suke neman fadada ayyukan ...

Musulmai Sun Yi Martani Ga Gumi Bayan Sukar Da Yayi Akan Maulud

Musulman Najeriya sun mamaye shafin Facebook na Dr. Ahmad Gumi. shahararren mai fafutukar kare hakkin ‘yan fashin daji bayan yayi suka ga maulidi a shafin a daidai lokacin da musulman suke  tunawa da ranar haihuwar Annabi Muhammad SAWA.  A kowace shekara a cikin watan Rabi’ul Awwal, Musulmin duniya suna tunawa da ranar haihuwar Annabi Muhammad ta hanyar karanta Alƙur’ani mai girma, ƙasidun yabo ya Annabi da karanta tarihin rayuwar sa. Shafin Dr. Gumi na Facebook ya samu sharhi sama da 600 har zuwa lokacin nan a tare da cewa suka yayi akan maulidin, amma da yawan su suna rubuta "Happy Maulud,"  duk da sun karanta sukar da yayi.   Karantarwar Dr Gumi tana fuskantar tsaiko da rashin tasiri akan mutane bayan ya karkatar da hankalin sa daga taimakon waɗanda rikicin yan fashin daji ya rutsa da su a arewa maso yammacin Najeriya zuwa neman haƙƙin masu aikata laifin.

Sanata Uba Sani ya Gina Makarantun ilimin fasahar Sadarwar zamani a mazabar sa

  A jihar kaduna A kokarin sa na Samar da ingantaccen ilimin zamani ga matasan ‘yan mazabarsa Sanata Uba Sani ya gina tare da samar da kayan aikin cibiyoyin Fasahar Sadarwar Zamani ICT a wasu kananan hukumomi cikin bakwai da Sanatan ke wakiltar a majalisar dattijan Nageriya An Samar da cibiyoyin ne a Makarantun da Suka ha’da da… 1. Maimuna Guarzo sakandirin gwamnatin dake Tudun Wada, a Kaduna ta Kudu, 2. Makarantar sakandaren gwamnati, Kawo, Kaduna ta Arewa da kuma 3. Makarantar sakandaren gwamnati, Turonku, karamar hukumar Igabi. (Ana Kan aiki) Samar da wannan makaratun zai ba wa malamai da ɗaliban Samun damar zama masu ilimin kwamfuta domin shiga jerin sahun sauran mutanen zamanin masu ilimin fasahar Zamani a duk matakan duniya. A Cikin ko wacce Makaranta an Samar da na’urori masu kwakwalwa (Computer) har guda ‘dari biyar 500, Jimulla dubu da ‘dari biyar 1,500. Ana sa ran Sanatan zai Samar da irin wannan makaratun a duk fa’din kananan hukumomin da yake wakilta a jihar kaduna. Anf...