Skip to main content

Sanata Uba Sani ya Gina Makarantun ilimin fasahar Sadarwar zamani a mazabar sa


A jihar kaduna A kokarin sa na Samar da ingantaccen ilimin zamani ga matasan ‘yan mazabarsa Sanata Uba Sani ya gina tare da samar da kayan aikin cibiyoyin Fasahar Sadarwar Zamani ICT a wasu kananan hukumomi cikin bakwai da Sanatan ke wakiltar a majalisar dattijan Nageriya

An Samar da cibiyoyin ne a Makarantun da Suka ha’da da…

1. Maimuna Guarzo sakandirin gwamnatin dake Tudun Wada, a Kaduna ta Kudu,

2. Makarantar sakandaren gwamnati, Kawo, Kaduna ta Arewa da kuma

3. Makarantar sakandaren gwamnati, Turonku, karamar hukumar Igabi. (Ana Kan aiki)

Samar da wannan makaratun zai ba wa malamai da ɗaliban Samun damar zama masu ilimin kwamfuta domin shiga jerin sahun sauran mutanen zamanin masu ilimin fasahar Zamani a duk matakan duniya.

A Cikin ko wacce Makaranta an Samar da na’urori masu kwakwalwa (Computer) har guda ‘dari biyar 500, Jimulla dubu da ‘dari biyar 1,500.

Ana sa ran Sanatan zai Samar da irin wannan makaratun a duk fa’din kananan hukumomin da yake wakilta a jihar kaduna.

Anfanin wannan cibiyoyi na
Fasahar Sadarwa (ICT) a cikin tsarin ilimi shine Samar da ilimi ta Hanyar amfani da fasahar sadarwa domin tallafawa da haɓaka hanyoyin isar da bayanai kala-kala a matakin Duniya.

Binciken duniya ya nuna cewa kafa Cibiyoyin ICT na iya haifar da ingantaccen tsarin ilmin ɗalibai da ingantattun hanyoyin koyarwa Cikin sauƙi, Rahoton da Cibiyar Ilimi ta Multimedia ta bayar a kasar Japan, ya tabbatar da cewa karuwar amfani da fasahar sadarwa ta ICT a cikin ilimi tare da hada fasahar da manhajar karatu yana da Matukar tasiri mai kyau da nagarta ga nasarorin dalibai musamman ɗaliban da ake ci gaba da Neman hanyoyin sanin ilmin fallasa su ta hanyar fasaha masu anfani da fasahar irin wannan cibiyoyi an kwatanta su Cewa basu da sa’a cikin tsarin fahimtar karatun Zamani.

Bincike ya tabbatar da cewa Rashin Ilimi na ‘daya daga cikin manya manyan Matsalolin dake saka matasa shiga harkokin ta’addanci, duba da Cewa jihar kaduna na ‘daya daga cikin Jihohin Arewa maso yamma dake fama da hare-haren ta’addancin ‘yan Bindiga, tabbas cigaba da Samar da ire-iren wannan cibiyoyi zai taimaka wajen dakile shigar matasa wannan harka ta ta’addanci.

Sanata Uba Sani na ‘daya daga Cikin Jerin ‘yan majalisar dattijan Nageriya dake kokarin ganin an raba matasa da Jahilci da Zaman banza ta hangar Samar da sana'o'i domin dogaro da kawunansu.

Comments

Popular posts from this blog

EFCC ta ƙaddamar da sabon salon yaƙi da rashawa a Najeriya

Shugaban EFCC Abdurrashid  Bawa Shugaban EFCC Abdulrasheed Bawa ya ce hukumar za ta fifita daƙile aikata laifuka kafin a aikata su Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta EFCC a Najeriya ta ce ta ɓullo da wani sabon salon daƙile ayyukan rashawa, inda za ta fi mayar da hankali kan rigakafin daƙile laifin kafin a aikata shi. A cewar Shugaban EFCC Abdulrasheed Bawa, daga yanzu hukumar za ta fi mayar da hankali wajen haɗa kai da abokan hulɗarta musamman na ƙasashen waje domin yaƙi da ayyukan rashawa. Da yake magana yayin taron ƙaddamar da sabon tsarin aikin a Abuja, Abdulrasheed Bawa ya ce sabon tsarin na 2021 zuwa 2025 an ciro shi ne daga kundin muradai na EFCC na shekarar 2013 zuwa 2018. "Sabon salon ya fi fifita rigakafi (hana faruwar laifi) a matsayin hanya mafi sauƙin daƙile rashawa fiye da yin hukunci," a cewarsa kamar yadda mujallar EFCC ta mako-mako ta ruwaito. Ya ƙara da cewa sabon tsarin zai fifita tattara bayanan sirri da gurfanar da masu laifi a gaban kotu...

Ganduje ya bai wa makaho aiki saboda bajintarsa

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya bai wa Ɗahuru Abdulhamid Idris wanda makaho ne, aikin koyarwa a gwamnatin jihar. Bayanin haka na ƙunshe ne cikin sanarwar da Sakataren Labarai na gwamnatin jihar, Abba Anwar ya fitar a ranar Lahadi. Kafin wannan lokaci, Ɗahuru ya kasance yana aikin koyarwa na sa-kai ba tare da ana biyansa wani albashi ba. Sanarwar ta ce bayan da Kwamishinan Ilimi na Jihar Kano, Muhammadu Sanusi Kiru, ya jagoranci Ɗahuru zuwa gaban Ganduje ne, a nan Ganduje ya bada umarnin a ɗauke shi aiki sannan a tura shi Makarantar Nakasassu da ke Tudun Maliki don ya ci gaba koyarwa. Yayin ganawar tasu, Ganduje ya yaba wa ƙoƙarin Ɗahuru musamman ma ganin yadda bai bari lalurar makanta ta hana shi bada tasa gudunmawa ga cigaban fannin ilimin jihar ba. Bisa wannan dalili ne Gwamna Ganduje ya ce, “Lallai ka taki matakin da ya dace a rayuwarka. Gwamnatin jihar Kano ta ba ka aikin koyarwa. Kuma na umarci Kwamishinan Ilimi da a tura ka zu...

PDP za ta 'Kwace mulki daga hannun APC a zaben 2023 - Inji Atiku Abubakar

Alh. Atiku Abubakar Tsohon mataimakin shugaban kasar Najeriya, Alhaji Atiku Abubakar ya bayyana kwarin gwiwar cewa jam'iyyar PDP, Mai adawa, za ta karbi mulki daga hannun jam'iyyar APC, mai mulki, a zaben shekarar 2023. Atku Abubakar ya bayyana hakan ne yayin da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan ya kada kuri'arsa a dandalin Mahmud Ribadu, Yola, wurin za'ben shugabannin  jam'iyyar PDP na jiha. Ya yi kira ga 'yan siyasa da su mutunta dokokin jam'iyya, na za'be, da Kuma na kundin tsarin mulkin kasar wajen zaben shugabannin jam'iyya, yana mai cewa dimokradiyya na iya 'dorewa ne a cikin yanayi na 'yanci da adalci