Skip to main content

Sanata Uba Sani ya Gina Makarantun ilimin fasahar Sadarwar zamani a mazabar sa


A jihar kaduna A kokarin sa na Samar da ingantaccen ilimin zamani ga matasan ‘yan mazabarsa Sanata Uba Sani ya gina tare da samar da kayan aikin cibiyoyin Fasahar Sadarwar Zamani ICT a wasu kananan hukumomi cikin bakwai da Sanatan ke wakiltar a majalisar dattijan Nageriya

An Samar da cibiyoyin ne a Makarantun da Suka ha’da da…

1. Maimuna Guarzo sakandirin gwamnatin dake Tudun Wada, a Kaduna ta Kudu,

2. Makarantar sakandaren gwamnati, Kawo, Kaduna ta Arewa da kuma

3. Makarantar sakandaren gwamnati, Turonku, karamar hukumar Igabi. (Ana Kan aiki)

Samar da wannan makaratun zai ba wa malamai da ɗaliban Samun damar zama masu ilimin kwamfuta domin shiga jerin sahun sauran mutanen zamanin masu ilimin fasahar Zamani a duk matakan duniya.

A Cikin ko wacce Makaranta an Samar da na’urori masu kwakwalwa (Computer) har guda ‘dari biyar 500, Jimulla dubu da ‘dari biyar 1,500.

Ana sa ran Sanatan zai Samar da irin wannan makaratun a duk fa’din kananan hukumomin da yake wakilta a jihar kaduna.

Anfanin wannan cibiyoyi na
Fasahar Sadarwa (ICT) a cikin tsarin ilimi shine Samar da ilimi ta Hanyar amfani da fasahar sadarwa domin tallafawa da haɓaka hanyoyin isar da bayanai kala-kala a matakin Duniya.

Binciken duniya ya nuna cewa kafa Cibiyoyin ICT na iya haifar da ingantaccen tsarin ilmin ɗalibai da ingantattun hanyoyin koyarwa Cikin sauƙi, Rahoton da Cibiyar Ilimi ta Multimedia ta bayar a kasar Japan, ya tabbatar da cewa karuwar amfani da fasahar sadarwa ta ICT a cikin ilimi tare da hada fasahar da manhajar karatu yana da Matukar tasiri mai kyau da nagarta ga nasarorin dalibai musamman ɗaliban da ake ci gaba da Neman hanyoyin sanin ilmin fallasa su ta hanyar fasaha masu anfani da fasahar irin wannan cibiyoyi an kwatanta su Cewa basu da sa’a cikin tsarin fahimtar karatun Zamani.

Bincike ya tabbatar da cewa Rashin Ilimi na ‘daya daga cikin manya manyan Matsalolin dake saka matasa shiga harkokin ta’addanci, duba da Cewa jihar kaduna na ‘daya daga cikin Jihohin Arewa maso yamma dake fama da hare-haren ta’addancin ‘yan Bindiga, tabbas cigaba da Samar da ire-iren wannan cibiyoyi zai taimaka wajen dakile shigar matasa wannan harka ta ta’addanci.

Sanata Uba Sani na ‘daya daga Cikin Jerin ‘yan majalisar dattijan Nageriya dake kokarin ganin an raba matasa da Jahilci da Zaman banza ta hangar Samar da sana'o'i domin dogaro da kawunansu.

Comments

Popular posts from this blog

Kamfanin Facebook Zai Canza Sunan Sa.

LABARU DA DUMI-DUMIN SU! Shahararren dandalin sada zumunta na Facebook Inc yana shirin sake sunan kansa da sabon suna a mako mai zuwa, shafin yanar gizo na fasahar Amurka Verge ya ruwaito a ranar Talata, inda ya ambaci wata majiya da ke da masaniya kai tsaye kan lamarin.  Babban Jami'i kuma Shugaban Facebook Mark Zuckerberg yana shirin yin magana game da canjin sunan a taron haɗin gwiwa na kamfani na shekara -shekara a ranar 28 ga Oktoba, amma ana iya bayyana shi da wuri, inji rahoton Verge. Labarin na zuwa ne a daidai lokacin da kamfanin ke fuskantar karuwar sanya ido daga gwamnati a Amurka kan harkokin kasuwancinsa.  Sake canza sunan zai sanya aikace -aikacen kafofin watsa labarun Facebook a matsayin ɗayan samfura da yawa a ƙarƙashin kamfanin, wanda kuma zai kula da sauran manhajojin sa kamar Instagram, WhatsApp, Oculus da sauran su, in ji rahoton Verge.  Ba sabon abu bane a Silicon Valley don kamfanoni sun canza sunayensu yayin da suke neman fadada ayyukan ...

Musulmai Sun Yi Martani Ga Gumi Bayan Sukar Da Yayi Akan Maulud

Musulman Najeriya sun mamaye shafin Facebook na Dr. Ahmad Gumi. shahararren mai fafutukar kare hakkin ‘yan fashin daji bayan yayi suka ga maulidi a shafin a daidai lokacin da musulman suke  tunawa da ranar haihuwar Annabi Muhammad SAWA.  A kowace shekara a cikin watan Rabi’ul Awwal, Musulmin duniya suna tunawa da ranar haihuwar Annabi Muhammad ta hanyar karanta Alƙur’ani mai girma, ƙasidun yabo ya Annabi da karanta tarihin rayuwar sa. Shafin Dr. Gumi na Facebook ya samu sharhi sama da 600 har zuwa lokacin nan a tare da cewa suka yayi akan maulidin, amma da yawan su suna rubuta "Happy Maulud,"  duk da sun karanta sukar da yayi.   Karantarwar Dr Gumi tana fuskantar tsaiko da rashin tasiri akan mutane bayan ya karkatar da hankalin sa daga taimakon waɗanda rikicin yan fashin daji ya rutsa da su a arewa maso yammacin Najeriya zuwa neman haƙƙin masu aikata laifin.