Skip to main content

Jerin sunayen 'yan Nigeria 11 da aka kama a Amurka kan almundahanar kudi da damfarar mutane fiye da 50


An kama wasu 'yan Nigeria 11 a Amurka bisa laifuka na almundahar kudade Laifukan da suka aikata sun hada da damfarar kamfanoni da mutane ta hanyar soyayya Masu bincike sun ce za a gurfanar da su a kotu domin su girbi abin da suka shuka, Hukumar binciken shari'a na Amurka ya gurfanar da wasu 'yan Nigeria 11 a kotu kan zarginsu da hada baki wurin aikata almundahar kudade, damfara ta banki da satar kudade da sunan wasu. A ranar Laraba ne Attoni na Kudancin New York, Damian Williams da Jam'in FBI mai kula da New York, Patrick J, Freancy suka sanar da sunayen 'yan Nigeria 11 da ke da hannu wurin karkatar da miliyoyin daloli daga damfarar imel da damfarar soyayya. 


EFCC Ta Gurfanar Da Yarima Gaban Kotu
EFCC ta gurfanar da Yarima a gaban kotu kan badakalar N35.5m 'Yan Nigeria 11 da aka gurfanar a Amurka kan almundahar kudi da damfarar mutane fiye da 50.

Hukumar binciken shari'a na Amurka ta bayyana hakan a ranar Laraba kamar yadda ya zo a ruwayar SaharaReporters.

An kama mutum tara cikinsu a New Jersey da Gabashin New York kuma za a gurfanar da su gaban Mai shari'a Sarah Netburn a Kudanci New York. Daya daga cikin wadanda ake zargin an kama shi ne a kudancin Texas kuma za a masa shari'a a kotun tarayya na yankin. Daya kuma har yanzu ana nemansa.

 Jerin sunayensu Wadanda ake zargi da almundahar kudin sune: 

1 Adedayo John 
2 Oluwadamilola Akinpelu
3 Kazeem Raheem 
4 Morakinyo Gbeyide 
5 Warris Adenuga, a.k.a 'Blue' 
6 Smart Agunbiade 
7 Lateef Goloba
8 Samsondeen Goloba 
9Olawale Olaniyan
0 Olawoyin Peter Olarewaju, da
1 Emmanuel Oronsaye-Ajayi 

An ruwaito Williams na cewa: 

"Kamar yadda ake tuhumarsu, wadanda aka kama suna cikin wata kungiyar bata gari da ke damfarar kamfanoni a intanet sannan suna damfarar dattawa ta hanyar yaudarar su da soyayya suna tura musu kudade, godiya ga 'yan sandan sirri na Secret Service, yanzu wadanda ake tuhuma suna kotu.

 Duk da komawa APC, da alamu Fani-Kayode zai fuskanci fushin kotu saboda badakala Freaney ya ce 'yan sandan na Secret Service za su cigaba da kare 'yan Amurka daga barazanar 'yan damfara masu yi wa kudadensu barazana kamar yadda SaharaReporters ta ruwaito.

'Yan Sanda Sunyi Ram Da Wani Sojan Gona
 ‘Yan sanda sun yi ram da wani sojan bogi, mai yi wa mata sata da sunan zai aure su A wani rahoton, ‘yan sanda sun kama Mkwatula mai shekaru 38 bisa yi wa tarin mata sata bayan dankara mu su karyar shi sojan Malawi ne kuma auren su ze yi bisa ruwayar LIB.

 Kakakin rundunar ‘yan sandan Ntcheu, Rabecca Kwisongole ta ce wanda ake zargin ya dade ya na yaudarar mata da soyayya da kuma alkawarin auren su. A cewar Kwisongole, bayan kwanaki da mika tayin soyayyar sa ga mace, Mkwatula zai lallaba ya sace mu su abubuwa masu daraja kamar babura, talabijin, wayoyi, barguna har kudade ma. 

Source: Legit.ng News

Comments

Popular posts from this blog

EFCC ta ƙaddamar da sabon salon yaƙi da rashawa a Najeriya

Shugaban EFCC Abdurrashid  Bawa Shugaban EFCC Abdulrasheed Bawa ya ce hukumar za ta fifita daƙile aikata laifuka kafin a aikata su Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta EFCC a Najeriya ta ce ta ɓullo da wani sabon salon daƙile ayyukan rashawa, inda za ta fi mayar da hankali kan rigakafin daƙile laifin kafin a aikata shi. A cewar Shugaban EFCC Abdulrasheed Bawa, daga yanzu hukumar za ta fi mayar da hankali wajen haɗa kai da abokan hulɗarta musamman na ƙasashen waje domin yaƙi da ayyukan rashawa. Da yake magana yayin taron ƙaddamar da sabon tsarin aikin a Abuja, Abdulrasheed Bawa ya ce sabon tsarin na 2021 zuwa 2025 an ciro shi ne daga kundin muradai na EFCC na shekarar 2013 zuwa 2018. "Sabon salon ya fi fifita rigakafi (hana faruwar laifi) a matsayin hanya mafi sauƙin daƙile rashawa fiye da yin hukunci," a cewarsa kamar yadda mujallar EFCC ta mako-mako ta ruwaito. Ya ƙara da cewa sabon tsarin zai fifita tattara bayanan sirri da gurfanar da masu laifi a gaban kotu...

Ganduje ya bai wa makaho aiki saboda bajintarsa

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya bai wa Ɗahuru Abdulhamid Idris wanda makaho ne, aikin koyarwa a gwamnatin jihar. Bayanin haka na ƙunshe ne cikin sanarwar da Sakataren Labarai na gwamnatin jihar, Abba Anwar ya fitar a ranar Lahadi. Kafin wannan lokaci, Ɗahuru ya kasance yana aikin koyarwa na sa-kai ba tare da ana biyansa wani albashi ba. Sanarwar ta ce bayan da Kwamishinan Ilimi na Jihar Kano, Muhammadu Sanusi Kiru, ya jagoranci Ɗahuru zuwa gaban Ganduje ne, a nan Ganduje ya bada umarnin a ɗauke shi aiki sannan a tura shi Makarantar Nakasassu da ke Tudun Maliki don ya ci gaba koyarwa. Yayin ganawar tasu, Ganduje ya yaba wa ƙoƙarin Ɗahuru musamman ma ganin yadda bai bari lalurar makanta ta hana shi bada tasa gudunmawa ga cigaban fannin ilimin jihar ba. Bisa wannan dalili ne Gwamna Ganduje ya ce, “Lallai ka taki matakin da ya dace a rayuwarka. Gwamnatin jihar Kano ta ba ka aikin koyarwa. Kuma na umarci Kwamishinan Ilimi da a tura ka zu...

PDP za ta 'Kwace mulki daga hannun APC a zaben 2023 - Inji Atiku Abubakar

Alh. Atiku Abubakar Tsohon mataimakin shugaban kasar Najeriya, Alhaji Atiku Abubakar ya bayyana kwarin gwiwar cewa jam'iyyar PDP, Mai adawa, za ta karbi mulki daga hannun jam'iyyar APC, mai mulki, a zaben shekarar 2023. Atku Abubakar ya bayyana hakan ne yayin da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan ya kada kuri'arsa a dandalin Mahmud Ribadu, Yola, wurin za'ben shugabannin  jam'iyyar PDP na jiha. Ya yi kira ga 'yan siyasa da su mutunta dokokin jam'iyya, na za'be, da Kuma na kundin tsarin mulkin kasar wajen zaben shugabannin jam'iyya, yana mai cewa dimokradiyya na iya 'dorewa ne a cikin yanayi na 'yanci da adalci