Skip to main content

Jerin sunayen 'yan Nigeria 11 da aka kama a Amurka kan almundahanar kudi da damfarar mutane fiye da 50


An kama wasu 'yan Nigeria 11 a Amurka bisa laifuka na almundahar kudade Laifukan da suka aikata sun hada da damfarar kamfanoni da mutane ta hanyar soyayya Masu bincike sun ce za a gurfanar da su a kotu domin su girbi abin da suka shuka, Hukumar binciken shari'a na Amurka ya gurfanar da wasu 'yan Nigeria 11 a kotu kan zarginsu da hada baki wurin aikata almundahar kudade, damfara ta banki da satar kudade da sunan wasu. A ranar Laraba ne Attoni na Kudancin New York, Damian Williams da Jam'in FBI mai kula da New York, Patrick J, Freancy suka sanar da sunayen 'yan Nigeria 11 da ke da hannu wurin karkatar da miliyoyin daloli daga damfarar imel da damfarar soyayya. 


EFCC Ta Gurfanar Da Yarima Gaban Kotu
EFCC ta gurfanar da Yarima a gaban kotu kan badakalar N35.5m 'Yan Nigeria 11 da aka gurfanar a Amurka kan almundahar kudi da damfarar mutane fiye da 50.

Hukumar binciken shari'a na Amurka ta bayyana hakan a ranar Laraba kamar yadda ya zo a ruwayar SaharaReporters.

An kama mutum tara cikinsu a New Jersey da Gabashin New York kuma za a gurfanar da su gaban Mai shari'a Sarah Netburn a Kudanci New York. Daya daga cikin wadanda ake zargin an kama shi ne a kudancin Texas kuma za a masa shari'a a kotun tarayya na yankin. Daya kuma har yanzu ana nemansa.

 Jerin sunayensu Wadanda ake zargi da almundahar kudin sune: 

1 Adedayo John 
2 Oluwadamilola Akinpelu
3 Kazeem Raheem 
4 Morakinyo Gbeyide 
5 Warris Adenuga, a.k.a 'Blue' 
6 Smart Agunbiade 
7 Lateef Goloba
8 Samsondeen Goloba 
9Olawale Olaniyan
0 Olawoyin Peter Olarewaju, da
1 Emmanuel Oronsaye-Ajayi 

An ruwaito Williams na cewa: 

"Kamar yadda ake tuhumarsu, wadanda aka kama suna cikin wata kungiyar bata gari da ke damfarar kamfanoni a intanet sannan suna damfarar dattawa ta hanyar yaudarar su da soyayya suna tura musu kudade, godiya ga 'yan sandan sirri na Secret Service, yanzu wadanda ake tuhuma suna kotu.

 Duk da komawa APC, da alamu Fani-Kayode zai fuskanci fushin kotu saboda badakala Freaney ya ce 'yan sandan na Secret Service za su cigaba da kare 'yan Amurka daga barazanar 'yan damfara masu yi wa kudadensu barazana kamar yadda SaharaReporters ta ruwaito.

'Yan Sanda Sunyi Ram Da Wani Sojan Gona
 ‘Yan sanda sun yi ram da wani sojan bogi, mai yi wa mata sata da sunan zai aure su A wani rahoton, ‘yan sanda sun kama Mkwatula mai shekaru 38 bisa yi wa tarin mata sata bayan dankara mu su karyar shi sojan Malawi ne kuma auren su ze yi bisa ruwayar LIB.

 Kakakin rundunar ‘yan sandan Ntcheu, Rabecca Kwisongole ta ce wanda ake zargin ya dade ya na yaudarar mata da soyayya da kuma alkawarin auren su. A cewar Kwisongole, bayan kwanaki da mika tayin soyayyar sa ga mace, Mkwatula zai lallaba ya sace mu su abubuwa masu daraja kamar babura, talabijin, wayoyi, barguna har kudade ma. 

Source: Legit.ng News

Comments

Popular posts from this blog

Buhari ya fusata da kisar gillar da aka yi wa masu cin kasuwa a garin Goronyo dake gabashin jihar Sokoto.

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yi matukar fusata da kisan gillar da aka yi wa masu cin Kasuwa a Goronyo, Jihar Sokoto inda ya aika wa ƴan bindiga sakon ‘Ta su ta kare’ ranar Litinin. Kakakin fadar shugaban ƙasa, Garba Shehu a wata takarda daga fadar shugaba Buhari ranar Litinin ya bayyana cewa shugaban Buhari ya fusata matuka da kisan da aka yi wa ƴan kasuwa da basu ji ba basu gani ba a kasuwar goronyo. Buhari ya ce wannan karon ƴan bindigan sun kai gwamnati maƙura kuma sun siya da kuɗin su domin sai sun gwammace kiɗa da karatu nan ba da daɗewa ba. ” Ko a yanzu ba su ji da daɗi daga dakarun Najeriya ta sama da kasa ba. Hakan yasa suke bin mutanen da basu ji ba basu gani suna kashe su. Wannan abu ya kai mu makura yanzu kuma lallai su kwana da shirin ta su ta kare. Harin Goronyo A kasuwar Goronyo jihar Sokoto dake ci mako-mako ne ‘yan bindiga suka buda wa mutane wuta inda suka kashe mutum sama da 30 sannan da dama sun ji rauni. Wannan hari ya auku ne kwanaki 12 da wasu ‘ya

Gwamnatin Kaduna ta ce an kashe mutum 343 cikin wata uku a jihar

Daga: Comrade Musa Garba Augie. Gwamnatin Jihar Kaduna ta tabbatar da mutuwar mutum 343 sakamakon ayyukan 'yan fashin daji da sauran tashe-tashen hankali cikin wata uku. Cikin wani rahoto da ya fitar ranar Laraba, Kwamashinan Tsaro da Harkokin Cikin Gida na Kaduna Samuel Aruwan ya bayyana cewa 'yan bindigar da ake zaton 'yan fashin daji ne sun sace mutum 830 a watannin. Rahoton ya duba rikice-rikicen da suka faru ne daga 1 ga watan Yuli zuwa 30 ga Satumban 2021. Sai dai rahoton ya nuna cewa adadin waɗanda aka sace a wata ukun ya ƙaru a kan na watannin Afrilu zuwa Yuni, inda aka sace 774 kuma aka kashe 222. •Na cire ɗana daga makarantar gwamnati saboda 'yan fashi na ƙoƙarin sace shi - El-Rufai •'Yan bindiga sun kai hari Makarantar Sojoji ta NDA •Abin da ya sa El-Rufai ba ya goyon bayan yin sulhu da ƴan bindiga •A gefe guda kuma, Mista Aruwan ya ce jami'an tsaro sun kashe jumillar 'yan fashi 69 a wurare daba-daban na jihar tare da tarwatsa sansanon

Sokoto: 'Ƴan bindiga sun kashe mutum 49 a kasuwar Goronyo'

Tambuwal Rahotanni daga jihar Sokoto a arewa maso yammacin Najeriya na cewa ƴan bidnga sun kashe aƙalla mutum 49 a wata kasuwa a garin Goronyo na jihar. Wasu ganau sun tabbatar wa da BBC labarin inda suka ce lamarin ya faru ne a ranar Lahadi da yamma, yayin da mutanen ke cin babbar kasuwar Goronyon. Mutanen waɗanda suka buƙaci a sakaya sunayensu saboda tsaro sun ce ƴan bindigar sun afka wa kasuwar ne a yayin da ta cika makil da masu hada-hada daga sassan jihar da ma wasu yankunan. "Ƴan fashin sun zo ne da misalin ƙarfe 4.30 zuwa biyar na yamma suka zagaye kasuwar suka buɗe wuta ta kowane ɓangare," in ji ganau ɗin. Majiyarmu ta yi ƙoƙarin jin ta bakin rund8nar ƴan sanda jihar, amma ba mu samu mai magana da yawun ƴan sanda ba a kiran waya da aka yi ta yi masa. Ya ƙara da cewa "Mutane duk suka ruɗe wasu sun kwakkwanta a ƙasa don gudun harbin ya same su, yayin da wasu suka gudu amma masu tsautsayi sun rasa rayukansu." Ganau ɗin sun ce an ƙidaya gawa 49 yayin