Skip to main content

Jerin sunayen 'yan Nigeria 11 da aka kama a Amurka kan almundahanar kudi da damfarar mutane fiye da 50


An kama wasu 'yan Nigeria 11 a Amurka bisa laifuka na almundahar kudade Laifukan da suka aikata sun hada da damfarar kamfanoni da mutane ta hanyar soyayya Masu bincike sun ce za a gurfanar da su a kotu domin su girbi abin da suka shuka, Hukumar binciken shari'a na Amurka ya gurfanar da wasu 'yan Nigeria 11 a kotu kan zarginsu da hada baki wurin aikata almundahar kudade, damfara ta banki da satar kudade da sunan wasu. A ranar Laraba ne Attoni na Kudancin New York, Damian Williams da Jam'in FBI mai kula da New York, Patrick J, Freancy suka sanar da sunayen 'yan Nigeria 11 da ke da hannu wurin karkatar da miliyoyin daloli daga damfarar imel da damfarar soyayya. 


EFCC Ta Gurfanar Da Yarima Gaban Kotu
EFCC ta gurfanar da Yarima a gaban kotu kan badakalar N35.5m 'Yan Nigeria 11 da aka gurfanar a Amurka kan almundahar kudi da damfarar mutane fiye da 50.

Hukumar binciken shari'a na Amurka ta bayyana hakan a ranar Laraba kamar yadda ya zo a ruwayar SaharaReporters.

An kama mutum tara cikinsu a New Jersey da Gabashin New York kuma za a gurfanar da su gaban Mai shari'a Sarah Netburn a Kudanci New York. Daya daga cikin wadanda ake zargin an kama shi ne a kudancin Texas kuma za a masa shari'a a kotun tarayya na yankin. Daya kuma har yanzu ana nemansa.

 Jerin sunayensu Wadanda ake zargi da almundahar kudin sune: 

1 Adedayo John 
2 Oluwadamilola Akinpelu
3 Kazeem Raheem 
4 Morakinyo Gbeyide 
5 Warris Adenuga, a.k.a 'Blue' 
6 Smart Agunbiade 
7 Lateef Goloba
8 Samsondeen Goloba 
9Olawale Olaniyan
0 Olawoyin Peter Olarewaju, da
1 Emmanuel Oronsaye-Ajayi 

An ruwaito Williams na cewa: 

"Kamar yadda ake tuhumarsu, wadanda aka kama suna cikin wata kungiyar bata gari da ke damfarar kamfanoni a intanet sannan suna damfarar dattawa ta hanyar yaudarar su da soyayya suna tura musu kudade, godiya ga 'yan sandan sirri na Secret Service, yanzu wadanda ake tuhuma suna kotu.

 Duk da komawa APC, da alamu Fani-Kayode zai fuskanci fushin kotu saboda badakala Freaney ya ce 'yan sandan na Secret Service za su cigaba da kare 'yan Amurka daga barazanar 'yan damfara masu yi wa kudadensu barazana kamar yadda SaharaReporters ta ruwaito.

'Yan Sanda Sunyi Ram Da Wani Sojan Gona
 ‘Yan sanda sun yi ram da wani sojan bogi, mai yi wa mata sata da sunan zai aure su A wani rahoton, ‘yan sanda sun kama Mkwatula mai shekaru 38 bisa yi wa tarin mata sata bayan dankara mu su karyar shi sojan Malawi ne kuma auren su ze yi bisa ruwayar LIB.

 Kakakin rundunar ‘yan sandan Ntcheu, Rabecca Kwisongole ta ce wanda ake zargin ya dade ya na yaudarar mata da soyayya da kuma alkawarin auren su. A cewar Kwisongole, bayan kwanaki da mika tayin soyayyar sa ga mace, Mkwatula zai lallaba ya sace mu su abubuwa masu daraja kamar babura, talabijin, wayoyi, barguna har kudade ma. 

Source: Legit.ng News

Comments

Popular posts from this blog

An Cafke Malamar Makarantar Da Ta Yiwa Yaro Ɗan Shekara 15 Fyaɗe

Wannan itace matar da hukumar 'yan sanda ke tuhuma da yiwa wani yaro Fyade. Bambarakwai, wai namiji da sunan Hajara,  Duk da Tuhumar da jami'ai ke yiwa matar, a bangare guda *yaron ya bayyana cewa ba fyaɗe ta mishi ba, da son rainsa suka yi lalata. An kama matar ne dauke da ciki niki-niki bayan da tawa wani ƙaramin yaro dan shekaru 15 fyaɗe. Matar mai suna Heiry Calvi dake karantarwa a makaranta dake Florida ta ƙasar Amurka na fuskantar tuhumar cin zarafin ƙaramin yaro. Sai dai yaron yace ba fyaɗe ta masa ba, da son ransa suka yi lalatar, amma an sanar da shi cewa doka bata yarda da hakan ba, har sai ya kai shekaru 18. An dai kasa tantance cikin na wanene, amma dai ƴan sanda sun kama matar suna bincike. Mu dai anan sadai muce... Can ga su Gada, Wai Zomo yaji kidan 'yan farauta.

Ganduje ya bai wa makaho aiki saboda bajintarsa

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya bai wa Ɗahuru Abdulhamid Idris wanda makaho ne, aikin koyarwa a gwamnatin jihar. Bayanin haka na ƙunshe ne cikin sanarwar da Sakataren Labarai na gwamnatin jihar, Abba Anwar ya fitar a ranar Lahadi. Kafin wannan lokaci, Ɗahuru ya kasance yana aikin koyarwa na sa-kai ba tare da ana biyansa wani albashi ba. Sanarwar ta ce bayan da Kwamishinan Ilimi na Jihar Kano, Muhammadu Sanusi Kiru, ya jagoranci Ɗahuru zuwa gaban Ganduje ne, a nan Ganduje ya bada umarnin a ɗauke shi aiki sannan a tura shi Makarantar Nakasassu da ke Tudun Maliki don ya ci gaba koyarwa. Yayin ganawar tasu, Ganduje ya yaba wa ƙoƙarin Ɗahuru musamman ma ganin yadda bai bari lalurar makanta ta hana shi bada tasa gudunmawa ga cigaban fannin ilimin jihar ba. Bisa wannan dalili ne Gwamna Ganduje ya ce, “Lallai ka taki matakin da ya dace a rayuwarka. Gwamnatin jihar Kano ta ba ka aikin koyarwa. Kuma na umarci Kwamishinan Ilimi da a tura ka zu...

Kamfanin Facebook Zai Canza Sunan Sa.

LABARU DA DUMI-DUMIN SU! Shahararren dandalin sada zumunta na Facebook Inc yana shirin sake sunan kansa da sabon suna a mako mai zuwa, shafin yanar gizo na fasahar Amurka Verge ya ruwaito a ranar Talata, inda ya ambaci wata majiya da ke da masaniya kai tsaye kan lamarin.  Babban Jami'i kuma Shugaban Facebook Mark Zuckerberg yana shirin yin magana game da canjin sunan a taron haɗin gwiwa na kamfani na shekara -shekara a ranar 28 ga Oktoba, amma ana iya bayyana shi da wuri, inji rahoton Verge. Labarin na zuwa ne a daidai lokacin da kamfanin ke fuskantar karuwar sanya ido daga gwamnati a Amurka kan harkokin kasuwancinsa.  Sake canza sunan zai sanya aikace -aikacen kafofin watsa labarun Facebook a matsayin ɗayan samfura da yawa a ƙarƙashin kamfanin, wanda kuma zai kula da sauran manhajojin sa kamar Instagram, WhatsApp, Oculus da sauran su, in ji rahoton Verge.  Ba sabon abu bane a Silicon Valley don kamfanoni sun canza sunayensu yayin da suke neman fadada ayyukan ...