Skip to main content

Jam'iyyar APC zata wargaje a Kano. Inji Shekarau


    Sen. Mal. Ibrahim Shekarau

Sakamakon rikicin da ya barke a jam'iyyar APC, Gwamnatin Kano karkashin jagorancin Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ta kira taron masu ruwa da tsaki na jam'iyyar

Gwamna Ganduje ya karanto sunayen mutanen da Gwamnatin Kano ta basu mukamai na jam'iyya a matakin jiha wanda zata tabbatar dasu gobe Asabar idan Allah Ya kaimh

A wajen taron da ya gabata jiya, Gwamna Ganduje ya keta alfarmar tsohon Gwamnan jihar Kano, kuma Sanatan Kano ta tsakiya, Malam Ibrahim Shekarau (Sardaunan Kano) inda ya kirashi da:
-Makaryaci
-Mai karbe-karbe
-Banza Bakwai

Hakika Gwamna Ganduje ya tafka babban kuskure da ya karbi shawaran miyagun da suke jikinsa har yake ganin zai iya ja da Malam Ibrahim Shekarau ya kai labari

A jihar Kano, bayan Sanata Rabiu Musa Kwankwaso babu wanda ya kai Malam Ibrahim Shekarau yawan masoya mabiya, nima Datti Assalafiy a dalilin Malam Ibrahim Shekarau na shigo yabon Gwamna Ganduje

Kuma na tabbata imba don Malam Ibrahim Shekarau ya zama sanadi ba, Wallahi zaben 2019 ba inda Gwamna Ganduje zai je, da bai kai labari ba, tabbas bai kamata a yiwa Malam Ibrahim Shekarau butulci ba

Lallai duk inda Malam Ibrahim Shekarau ya nufa zamu bishi, kuma muna tare dashi a kowace jam'iyya na siyasa

Allah Ka daukaka darajar Malam Ibrahim Shekarau

Zubin rubutu: Salisu Idris Waziri

Comments

Popular posts from this blog

An Cafke Malamar Makarantar Da Ta Yiwa Yaro Ɗan Shekara 15 Fyaɗe

Wannan itace matar da hukumar 'yan sanda ke tuhuma da yiwa wani yaro Fyade. Bambarakwai, wai namiji da sunan Hajara,  Duk da Tuhumar da jami'ai ke yiwa matar, a bangare guda *yaron ya bayyana cewa ba fyaɗe ta mishi ba, da son rainsa suka yi lalata. An kama matar ne dauke da ciki niki-niki bayan da tawa wani ƙaramin yaro dan shekaru 15 fyaɗe. Matar mai suna Heiry Calvi dake karantarwa a makaranta dake Florida ta ƙasar Amurka na fuskantar tuhumar cin zarafin ƙaramin yaro. Sai dai yaron yace ba fyaɗe ta masa ba, da son ransa suka yi lalatar, amma an sanar da shi cewa doka bata yarda da hakan ba, har sai ya kai shekaru 18. An dai kasa tantance cikin na wanene, amma dai ƴan sanda sun kama matar suna bincike. Mu dai anan sadai muce... Can ga su Gada, Wai Zomo yaji kidan 'yan farauta.

Ganduje ya bai wa makaho aiki saboda bajintarsa

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya bai wa Ɗahuru Abdulhamid Idris wanda makaho ne, aikin koyarwa a gwamnatin jihar. Bayanin haka na ƙunshe ne cikin sanarwar da Sakataren Labarai na gwamnatin jihar, Abba Anwar ya fitar a ranar Lahadi. Kafin wannan lokaci, Ɗahuru ya kasance yana aikin koyarwa na sa-kai ba tare da ana biyansa wani albashi ba. Sanarwar ta ce bayan da Kwamishinan Ilimi na Jihar Kano, Muhammadu Sanusi Kiru, ya jagoranci Ɗahuru zuwa gaban Ganduje ne, a nan Ganduje ya bada umarnin a ɗauke shi aiki sannan a tura shi Makarantar Nakasassu da ke Tudun Maliki don ya ci gaba koyarwa. Yayin ganawar tasu, Ganduje ya yaba wa ƙoƙarin Ɗahuru musamman ma ganin yadda bai bari lalurar makanta ta hana shi bada tasa gudunmawa ga cigaban fannin ilimin jihar ba. Bisa wannan dalili ne Gwamna Ganduje ya ce, “Lallai ka taki matakin da ya dace a rayuwarka. Gwamnatin jihar Kano ta ba ka aikin koyarwa. Kuma na umarci Kwamishinan Ilimi da a tura ka zu...

Kamfanin Facebook Zai Canza Sunan Sa.

LABARU DA DUMI-DUMIN SU! Shahararren dandalin sada zumunta na Facebook Inc yana shirin sake sunan kansa da sabon suna a mako mai zuwa, shafin yanar gizo na fasahar Amurka Verge ya ruwaito a ranar Talata, inda ya ambaci wata majiya da ke da masaniya kai tsaye kan lamarin.  Babban Jami'i kuma Shugaban Facebook Mark Zuckerberg yana shirin yin magana game da canjin sunan a taron haɗin gwiwa na kamfani na shekara -shekara a ranar 28 ga Oktoba, amma ana iya bayyana shi da wuri, inji rahoton Verge. Labarin na zuwa ne a daidai lokacin da kamfanin ke fuskantar karuwar sanya ido daga gwamnati a Amurka kan harkokin kasuwancinsa.  Sake canza sunan zai sanya aikace -aikacen kafofin watsa labarun Facebook a matsayin ɗayan samfura da yawa a ƙarƙashin kamfanin, wanda kuma zai kula da sauran manhajojin sa kamar Instagram, WhatsApp, Oculus da sauran su, in ji rahoton Verge.  Ba sabon abu bane a Silicon Valley don kamfanoni sun canza sunayensu yayin da suke neman fadada ayyukan ...