Sakamakon rikicin da ya barke a jam'iyyar APC, Gwamnatin Kano karkashin jagorancin Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ta kira taron masu ruwa da tsaki na jam'iyyar
Gwamna Ganduje ya karanto sunayen mutanen da Gwamnatin Kano ta basu mukamai na jam'iyya a matakin jiha wanda zata tabbatar dasu gobe Asabar idan Allah Ya kaimh
A wajen taron da ya gabata jiya, Gwamna Ganduje ya keta alfarmar tsohon Gwamnan jihar Kano, kuma Sanatan Kano ta tsakiya, Malam Ibrahim Shekarau (Sardaunan Kano) inda ya kirashi da:
-Makaryaci
-Mai karbe-karbe
-Banza Bakwai
Hakika Gwamna Ganduje ya tafka babban kuskure da ya karbi shawaran miyagun da suke jikinsa har yake ganin zai iya ja da Malam Ibrahim Shekarau ya kai labari
A jihar Kano, bayan Sanata Rabiu Musa Kwankwaso babu wanda ya kai Malam Ibrahim Shekarau yawan masoya mabiya, nima Datti Assalafiy a dalilin Malam Ibrahim Shekarau na shigo yabon Gwamna Ganduje
Kuma na tabbata imba don Malam Ibrahim Shekarau ya zama sanadi ba, Wallahi zaben 2019 ba inda Gwamna Ganduje zai je, da bai kai labari ba, tabbas bai kamata a yiwa Malam Ibrahim Shekarau butulci ba
Lallai duk inda Malam Ibrahim Shekarau ya nufa zamu bishi, kuma muna tare dashi a kowace jam'iyya na siyasa
Allah Ka daukaka darajar Malam Ibrahim Shekarau
Zubin rubutu: Salisu Idris Waziri
Comments
Post a Comment