Skip to main content

Harin Goronyo: 'Yadda muka riƙa kutsawa gidajen matan aure don tsira '



Yan bindiga


Ƴan uwa da abokar arziƙin mutanen nan 30 zuwa 60 da suka gamu da ajalinsu yayin wani harin ƴan fashin daji a garin Goronyo da ke jihar Sokoto na ci gaba da jimamin rashin ƴan uwan na su.

Kamar yadda mane labarai suka tattauna da wasu mazauna garin, inda suka bayyana halin da suka shiga, a lokacin da mahran suka yi wa garin kofar rago tare da buɗe wuta kan mai uwa da wabi.

Wani mutum da muka sakaye sunansa, ya ce bai taba ganin tashin hankali a rayuwarsa irin wannan ba, domin ta kai hatta katangar gidan da yake tana jijjiga saboda yadda harbi ya karade gari ko ta ina.

"Ina zaune tare da mutane kawai sai muka ji ana barin wuta, aka ce ai ɓarayi ne, karfe 4:30 na maraice, daga nan kuma muka tashi muka ruga da gudu, muka tsallake katanga muka fada wani gida, ko ina barin wuta ake, ba su tafi ba sai ƙarfe shidda, sannan suka hau baburansu suka wuce.

A cewar wannan mutumin, Allah ne kawai bai sa kwanansa ya ƙare ba, amma ba don haka ba da tuni shi ma yana cikin mutanen da suka mutu.

''Bayan sun tafi ko da na fito sun kashe mutum mutum hudu a bayan gidan da na ɓuya, duka gari dai ya ruɗe kowa yana biɗar ƴan uwansa, abin dai babu daɗin gani ko kadan'' inji wannan shaida, a zantawarsa da tashar BBC

Mutum 20 a dakin matar aure

Taswirar jhar Sokoto

Shi ma wani shaida da muka sakaye sunansa da ke zaune a garin na Goronyo, ya ce kasuwar garin da aka kai harin bata taba cika tun da aka fara damuna kamar ranar da aka kai wannan farmaki da ya janyo mutuwar kimanin mutane 50 ba.

''Ina kusa da asibiti ban ji komai ba sai karar bindiga na tashi, ashe sun kewaye ko ina, da jin haka kuwa sai kowa ya kama gabansa, haka muka yi ta kutsawa gidajen matan aure, sai ka ga muum 20 a dakin matar aure, kuma a gaji a kulle haka nan'' inji shi.

A cewarsa 'an kashe mutum 7 cikin ƴan kato da gorar da suka yi kokarin tunkarar 'yan fashin dajin domin dakile su kafin su far wa jama'ar gari da suke kokarin tunkara.

Abin da Buhari ya ce kan batun

Buhari


Shi dai Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya ce lokaci na gab da zuwa ƙarshe ga mummunar ɓarnar da 'yan fashin fashin daji ke haddasawa musamman a yankin arewacin ƙasar.

Muhammadu Buhari na wannan jawabi ne a cikin wata sanarwa da ya fitar don juyayin mummunan harin da aka kai kan kasuwar Goronyo wadda ta cika maƙil, inda majiyoyi ke cewa an kashe kimanin mutum 30 zuwa 60 yayin harin na ranar Lahadi.

Ya dai yi kira ga 'yan ƙasar da kada su karaya, maimakon haka su ci gaba da haƙuri don kuwa hukumomi sun duƙufa fiye da kowanne lokaci a baya wajen kare 'yan Najeriya da kuma murƙushe gungun masu ɗauke da makamai.

Comments

Popular posts from this blog

Kamfanin Facebook Zai Canza Sunan Sa.

LABARU DA DUMI-DUMIN SU! Shahararren dandalin sada zumunta na Facebook Inc yana shirin sake sunan kansa da sabon suna a mako mai zuwa, shafin yanar gizo na fasahar Amurka Verge ya ruwaito a ranar Talata, inda ya ambaci wata majiya da ke da masaniya kai tsaye kan lamarin.  Babban Jami'i kuma Shugaban Facebook Mark Zuckerberg yana shirin yin magana game da canjin sunan a taron haɗin gwiwa na kamfani na shekara -shekara a ranar 28 ga Oktoba, amma ana iya bayyana shi da wuri, inji rahoton Verge. Labarin na zuwa ne a daidai lokacin da kamfanin ke fuskantar karuwar sanya ido daga gwamnati a Amurka kan harkokin kasuwancinsa.  Sake canza sunan zai sanya aikace -aikacen kafofin watsa labarun Facebook a matsayin ɗayan samfura da yawa a ƙarƙashin kamfanin, wanda kuma zai kula da sauran manhajojin sa kamar Instagram, WhatsApp, Oculus da sauran su, in ji rahoton Verge.  Ba sabon abu bane a Silicon Valley don kamfanoni sun canza sunayensu yayin da suke neman fadada ayyukan ...

Musulmai Sun Yi Martani Ga Gumi Bayan Sukar Da Yayi Akan Maulud

Musulman Najeriya sun mamaye shafin Facebook na Dr. Ahmad Gumi. shahararren mai fafutukar kare hakkin ‘yan fashin daji bayan yayi suka ga maulidi a shafin a daidai lokacin da musulman suke  tunawa da ranar haihuwar Annabi Muhammad SAWA.  A kowace shekara a cikin watan Rabi’ul Awwal, Musulmin duniya suna tunawa da ranar haihuwar Annabi Muhammad ta hanyar karanta Alƙur’ani mai girma, ƙasidun yabo ya Annabi da karanta tarihin rayuwar sa. Shafin Dr. Gumi na Facebook ya samu sharhi sama da 600 har zuwa lokacin nan a tare da cewa suka yayi akan maulidin, amma da yawan su suna rubuta "Happy Maulud,"  duk da sun karanta sukar da yayi.   Karantarwar Dr Gumi tana fuskantar tsaiko da rashin tasiri akan mutane bayan ya karkatar da hankalin sa daga taimakon waɗanda rikicin yan fashin daji ya rutsa da su a arewa maso yammacin Najeriya zuwa neman haƙƙin masu aikata laifin.

Sanata Uba Sani ya Gina Makarantun ilimin fasahar Sadarwar zamani a mazabar sa

  A jihar kaduna A kokarin sa na Samar da ingantaccen ilimin zamani ga matasan ‘yan mazabarsa Sanata Uba Sani ya gina tare da samar da kayan aikin cibiyoyin Fasahar Sadarwar Zamani ICT a wasu kananan hukumomi cikin bakwai da Sanatan ke wakiltar a majalisar dattijan Nageriya An Samar da cibiyoyin ne a Makarantun da Suka ha’da da… 1. Maimuna Guarzo sakandirin gwamnatin dake Tudun Wada, a Kaduna ta Kudu, 2. Makarantar sakandaren gwamnati, Kawo, Kaduna ta Arewa da kuma 3. Makarantar sakandaren gwamnati, Turonku, karamar hukumar Igabi. (Ana Kan aiki) Samar da wannan makaratun zai ba wa malamai da ɗaliban Samun damar zama masu ilimin kwamfuta domin shiga jerin sahun sauran mutanen zamanin masu ilimin fasahar Zamani a duk matakan duniya. A Cikin ko wacce Makaranta an Samar da na’urori masu kwakwalwa (Computer) har guda ‘dari biyar 500, Jimulla dubu da ‘dari biyar 1,500. Ana sa ran Sanatan zai Samar da irin wannan makaratun a duk fa’din kananan hukumomin da yake wakilta a jihar kaduna. Anf...