Skip to main content

Harin Goronyo: 'Yadda muka riƙa kutsawa gidajen matan aure don tsira '



Yan bindiga


Ƴan uwa da abokar arziƙin mutanen nan 30 zuwa 60 da suka gamu da ajalinsu yayin wani harin ƴan fashin daji a garin Goronyo da ke jihar Sokoto na ci gaba da jimamin rashin ƴan uwan na su.

Kamar yadda mane labarai suka tattauna da wasu mazauna garin, inda suka bayyana halin da suka shiga, a lokacin da mahran suka yi wa garin kofar rago tare da buɗe wuta kan mai uwa da wabi.

Wani mutum da muka sakaye sunansa, ya ce bai taba ganin tashin hankali a rayuwarsa irin wannan ba, domin ta kai hatta katangar gidan da yake tana jijjiga saboda yadda harbi ya karade gari ko ta ina.

"Ina zaune tare da mutane kawai sai muka ji ana barin wuta, aka ce ai ɓarayi ne, karfe 4:30 na maraice, daga nan kuma muka tashi muka ruga da gudu, muka tsallake katanga muka fada wani gida, ko ina barin wuta ake, ba su tafi ba sai ƙarfe shidda, sannan suka hau baburansu suka wuce.

A cewar wannan mutumin, Allah ne kawai bai sa kwanansa ya ƙare ba, amma ba don haka ba da tuni shi ma yana cikin mutanen da suka mutu.

''Bayan sun tafi ko da na fito sun kashe mutum mutum hudu a bayan gidan da na ɓuya, duka gari dai ya ruɗe kowa yana biɗar ƴan uwansa, abin dai babu daɗin gani ko kadan'' inji wannan shaida, a zantawarsa da tashar BBC

Mutum 20 a dakin matar aure

Taswirar jhar Sokoto

Shi ma wani shaida da muka sakaye sunansa da ke zaune a garin na Goronyo, ya ce kasuwar garin da aka kai harin bata taba cika tun da aka fara damuna kamar ranar da aka kai wannan farmaki da ya janyo mutuwar kimanin mutane 50 ba.

''Ina kusa da asibiti ban ji komai ba sai karar bindiga na tashi, ashe sun kewaye ko ina, da jin haka kuwa sai kowa ya kama gabansa, haka muka yi ta kutsawa gidajen matan aure, sai ka ga muum 20 a dakin matar aure, kuma a gaji a kulle haka nan'' inji shi.

A cewarsa 'an kashe mutum 7 cikin ƴan kato da gorar da suka yi kokarin tunkarar 'yan fashin dajin domin dakile su kafin su far wa jama'ar gari da suke kokarin tunkara.

Abin da Buhari ya ce kan batun

Buhari


Shi dai Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya ce lokaci na gab da zuwa ƙarshe ga mummunar ɓarnar da 'yan fashin fashin daji ke haddasawa musamman a yankin arewacin ƙasar.

Muhammadu Buhari na wannan jawabi ne a cikin wata sanarwa da ya fitar don juyayin mummunan harin da aka kai kan kasuwar Goronyo wadda ta cika maƙil, inda majiyoyi ke cewa an kashe kimanin mutum 30 zuwa 60 yayin harin na ranar Lahadi.

Ya dai yi kira ga 'yan ƙasar da kada su karaya, maimakon haka su ci gaba da haƙuri don kuwa hukumomi sun duƙufa fiye da kowanne lokaci a baya wajen kare 'yan Najeriya da kuma murƙushe gungun masu ɗauke da makamai.

Comments

Popular posts from this blog

Buhari ya fusata da kisar gillar da aka yi wa masu cin kasuwa a garin Goronyo dake gabashin jihar Sokoto.

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yi matukar fusata da kisan gillar da aka yi wa masu cin Kasuwa a Goronyo, Jihar Sokoto inda ya aika wa ƴan bindiga sakon ‘Ta su ta kare’ ranar Litinin. Kakakin fadar shugaban ƙasa, Garba Shehu a wata takarda daga fadar shugaba Buhari ranar Litinin ya bayyana cewa shugaban Buhari ya fusata matuka da kisan da aka yi wa ƴan kasuwa da basu ji ba basu gani ba a kasuwar goronyo. Buhari ya ce wannan karon ƴan bindigan sun kai gwamnati maƙura kuma sun siya da kuɗin su domin sai sun gwammace kiɗa da karatu nan ba da daɗewa ba. ” Ko a yanzu ba su ji da daɗi daga dakarun Najeriya ta sama da kasa ba. Hakan yasa suke bin mutanen da basu ji ba basu gani suna kashe su. Wannan abu ya kai mu makura yanzu kuma lallai su kwana da shirin ta su ta kare. Harin Goronyo A kasuwar Goronyo jihar Sokoto dake ci mako-mako ne ‘yan bindiga suka buda wa mutane wuta inda suka kashe mutum sama da 30 sannan da dama sun ji rauni. Wannan hari ya auku ne kwanaki 12 da wasu ‘ya

Gwamnatin Kaduna ta ce an kashe mutum 343 cikin wata uku a jihar

Daga: Comrade Musa Garba Augie. Gwamnatin Jihar Kaduna ta tabbatar da mutuwar mutum 343 sakamakon ayyukan 'yan fashin daji da sauran tashe-tashen hankali cikin wata uku. Cikin wani rahoto da ya fitar ranar Laraba, Kwamashinan Tsaro da Harkokin Cikin Gida na Kaduna Samuel Aruwan ya bayyana cewa 'yan bindigar da ake zaton 'yan fashin daji ne sun sace mutum 830 a watannin. Rahoton ya duba rikice-rikicen da suka faru ne daga 1 ga watan Yuli zuwa 30 ga Satumban 2021. Sai dai rahoton ya nuna cewa adadin waɗanda aka sace a wata ukun ya ƙaru a kan na watannin Afrilu zuwa Yuni, inda aka sace 774 kuma aka kashe 222. •Na cire ɗana daga makarantar gwamnati saboda 'yan fashi na ƙoƙarin sace shi - El-Rufai •'Yan bindiga sun kai hari Makarantar Sojoji ta NDA •Abin da ya sa El-Rufai ba ya goyon bayan yin sulhu da ƴan bindiga •A gefe guda kuma, Mista Aruwan ya ce jami'an tsaro sun kashe jumillar 'yan fashi 69 a wurare daba-daban na jihar tare da tarwatsa sansanon

Sokoto: 'Ƴan bindiga sun kashe mutum 49 a kasuwar Goronyo'

Tambuwal Rahotanni daga jihar Sokoto a arewa maso yammacin Najeriya na cewa ƴan bidnga sun kashe aƙalla mutum 49 a wata kasuwa a garin Goronyo na jihar. Wasu ganau sun tabbatar wa da BBC labarin inda suka ce lamarin ya faru ne a ranar Lahadi da yamma, yayin da mutanen ke cin babbar kasuwar Goronyon. Mutanen waɗanda suka buƙaci a sakaya sunayensu saboda tsaro sun ce ƴan bindigar sun afka wa kasuwar ne a yayin da ta cika makil da masu hada-hada daga sassan jihar da ma wasu yankunan. "Ƴan fashin sun zo ne da misalin ƙarfe 4.30 zuwa biyar na yamma suka zagaye kasuwar suka buɗe wuta ta kowane ɓangare," in ji ganau ɗin. Majiyarmu ta yi ƙoƙarin jin ta bakin rund8nar ƴan sanda jihar, amma ba mu samu mai magana da yawun ƴan sanda ba a kiran waya da aka yi ta yi masa. Ya ƙara da cewa "Mutane duk suka ruɗe wasu sun kwakkwanta a ƙasa don gudun harbin ya same su, yayin da wasu suka gudu amma masu tsautsayi sun rasa rayukansu." Ganau ɗin sun ce an ƙidaya gawa 49 yayin