Skip to main content

Harin Goronyo: 'Yadda muka riƙa kutsawa gidajen matan aure don tsira '



Yan bindiga


Ƴan uwa da abokar arziƙin mutanen nan 30 zuwa 60 da suka gamu da ajalinsu yayin wani harin ƴan fashin daji a garin Goronyo da ke jihar Sokoto na ci gaba da jimamin rashin ƴan uwan na su.

Kamar yadda mane labarai suka tattauna da wasu mazauna garin, inda suka bayyana halin da suka shiga, a lokacin da mahran suka yi wa garin kofar rago tare da buɗe wuta kan mai uwa da wabi.

Wani mutum da muka sakaye sunansa, ya ce bai taba ganin tashin hankali a rayuwarsa irin wannan ba, domin ta kai hatta katangar gidan da yake tana jijjiga saboda yadda harbi ya karade gari ko ta ina.

"Ina zaune tare da mutane kawai sai muka ji ana barin wuta, aka ce ai ɓarayi ne, karfe 4:30 na maraice, daga nan kuma muka tashi muka ruga da gudu, muka tsallake katanga muka fada wani gida, ko ina barin wuta ake, ba su tafi ba sai ƙarfe shidda, sannan suka hau baburansu suka wuce.

A cewar wannan mutumin, Allah ne kawai bai sa kwanansa ya ƙare ba, amma ba don haka ba da tuni shi ma yana cikin mutanen da suka mutu.

''Bayan sun tafi ko da na fito sun kashe mutum mutum hudu a bayan gidan da na ɓuya, duka gari dai ya ruɗe kowa yana biɗar ƴan uwansa, abin dai babu daɗin gani ko kadan'' inji wannan shaida, a zantawarsa da tashar BBC

Mutum 20 a dakin matar aure

Taswirar jhar Sokoto

Shi ma wani shaida da muka sakaye sunansa da ke zaune a garin na Goronyo, ya ce kasuwar garin da aka kai harin bata taba cika tun da aka fara damuna kamar ranar da aka kai wannan farmaki da ya janyo mutuwar kimanin mutane 50 ba.

''Ina kusa da asibiti ban ji komai ba sai karar bindiga na tashi, ashe sun kewaye ko ina, da jin haka kuwa sai kowa ya kama gabansa, haka muka yi ta kutsawa gidajen matan aure, sai ka ga muum 20 a dakin matar aure, kuma a gaji a kulle haka nan'' inji shi.

A cewarsa 'an kashe mutum 7 cikin ƴan kato da gorar da suka yi kokarin tunkarar 'yan fashin dajin domin dakile su kafin su far wa jama'ar gari da suke kokarin tunkara.

Abin da Buhari ya ce kan batun

Buhari


Shi dai Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya ce lokaci na gab da zuwa ƙarshe ga mummunar ɓarnar da 'yan fashin fashin daji ke haddasawa musamman a yankin arewacin ƙasar.

Muhammadu Buhari na wannan jawabi ne a cikin wata sanarwa da ya fitar don juyayin mummunan harin da aka kai kan kasuwar Goronyo wadda ta cika maƙil, inda majiyoyi ke cewa an kashe kimanin mutum 30 zuwa 60 yayin harin na ranar Lahadi.

Ya dai yi kira ga 'yan ƙasar da kada su karaya, maimakon haka su ci gaba da haƙuri don kuwa hukumomi sun duƙufa fiye da kowanne lokaci a baya wajen kare 'yan Najeriya da kuma murƙushe gungun masu ɗauke da makamai.

Comments

Popular posts from this blog

EFCC ta ƙaddamar da sabon salon yaƙi da rashawa a Najeriya

Shugaban EFCC Abdurrashid  Bawa Shugaban EFCC Abdulrasheed Bawa ya ce hukumar za ta fifita daƙile aikata laifuka kafin a aikata su Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta EFCC a Najeriya ta ce ta ɓullo da wani sabon salon daƙile ayyukan rashawa, inda za ta fi mayar da hankali kan rigakafin daƙile laifin kafin a aikata shi. A cewar Shugaban EFCC Abdulrasheed Bawa, daga yanzu hukumar za ta fi mayar da hankali wajen haɗa kai da abokan hulɗarta musamman na ƙasashen waje domin yaƙi da ayyukan rashawa. Da yake magana yayin taron ƙaddamar da sabon tsarin aikin a Abuja, Abdulrasheed Bawa ya ce sabon tsarin na 2021 zuwa 2025 an ciro shi ne daga kundin muradai na EFCC na shekarar 2013 zuwa 2018. "Sabon salon ya fi fifita rigakafi (hana faruwar laifi) a matsayin hanya mafi sauƙin daƙile rashawa fiye da yin hukunci," a cewarsa kamar yadda mujallar EFCC ta mako-mako ta ruwaito. Ya ƙara da cewa sabon tsarin zai fifita tattara bayanan sirri da gurfanar da masu laifi a gaban kotu...

Ganduje ya bai wa makaho aiki saboda bajintarsa

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya bai wa Ɗahuru Abdulhamid Idris wanda makaho ne, aikin koyarwa a gwamnatin jihar. Bayanin haka na ƙunshe ne cikin sanarwar da Sakataren Labarai na gwamnatin jihar, Abba Anwar ya fitar a ranar Lahadi. Kafin wannan lokaci, Ɗahuru ya kasance yana aikin koyarwa na sa-kai ba tare da ana biyansa wani albashi ba. Sanarwar ta ce bayan da Kwamishinan Ilimi na Jihar Kano, Muhammadu Sanusi Kiru, ya jagoranci Ɗahuru zuwa gaban Ganduje ne, a nan Ganduje ya bada umarnin a ɗauke shi aiki sannan a tura shi Makarantar Nakasassu da ke Tudun Maliki don ya ci gaba koyarwa. Yayin ganawar tasu, Ganduje ya yaba wa ƙoƙarin Ɗahuru musamman ma ganin yadda bai bari lalurar makanta ta hana shi bada tasa gudunmawa ga cigaban fannin ilimin jihar ba. Bisa wannan dalili ne Gwamna Ganduje ya ce, “Lallai ka taki matakin da ya dace a rayuwarka. Gwamnatin jihar Kano ta ba ka aikin koyarwa. Kuma na umarci Kwamishinan Ilimi da a tura ka zu...

PDP za ta 'Kwace mulki daga hannun APC a zaben 2023 - Inji Atiku Abubakar

Alh. Atiku Abubakar Tsohon mataimakin shugaban kasar Najeriya, Alhaji Atiku Abubakar ya bayyana kwarin gwiwar cewa jam'iyyar PDP, Mai adawa, za ta karbi mulki daga hannun jam'iyyar APC, mai mulki, a zaben shekarar 2023. Atku Abubakar ya bayyana hakan ne yayin da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan ya kada kuri'arsa a dandalin Mahmud Ribadu, Yola, wurin za'ben shugabannin  jam'iyyar PDP na jiha. Ya yi kira ga 'yan siyasa da su mutunta dokokin jam'iyya, na za'be, da Kuma na kundin tsarin mulkin kasar wajen zaben shugabannin jam'iyya, yana mai cewa dimokradiyya na iya 'dorewa ne a cikin yanayi na 'yanci da adalci