Skip to main content

EFCC ta ƙaddamar da sabon salon yaƙi da rashawa a Najeriya



Shugaban EFCC Abdurrashid Bawa

Shugaban EFCC Abdulrasheed Bawa ya ce hukumar za ta fifita daƙile aikata laifuka kafin a aikata su
Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta EFCC a Najeriya ta ce ta ɓullo da wani sabon salon daƙile ayyukan rashawa, inda za ta fi mayar da hankali kan rigakafin daƙile laifin kafin a aikata shi.

A cewar Shugaban EFCC Abdulrasheed Bawa, daga yanzu hukumar za ta fi mayar da hankali wajen haɗa kai da abokan hulɗarta musamman na ƙasashen waje domin yaƙi da ayyukan rashawa.

Da yake magana yayin taron ƙaddamar da sabon tsarin aikin a Abuja, Abdulrasheed Bawa ya ce sabon tsarin na 2021 zuwa 2025 an ciro shi ne daga kundin muradai na EFCC na shekarar 2013 zuwa 2018.
"Sabon salon ya fi fifita rigakafi (hana faruwar laifi) a matsayin hanya mafi sauƙin daƙile rashawa fiye da yin hukunci," a cewarsa kamar yadda mujallar EFCC ta mako-mako ta ruwaito.

Ya ƙara da cewa sabon tsarin zai fifita tattara bayanan sirri da gurfanar da masu laifi a gaban kotu ta hanyar kyautata tsarin aiki.
A watan Yulin 2021 EFCC ta kaddamar da wata manhaja da za ta bai wa 'yan kasa damar ɗaukar hotunan abubuwa ko wuraren da ake aikata laifuka da zummar aika mata da bayanan.

Manyan jami'an Najeriya shida da suka yanke jiki suka faɗi yayin tuhumarsu
An yanke wa ɗan Abdulrasheed Maina hukuncin ɗaurin shekara 24
Muradi biyar
Kundin EFCC.


Sabon kundin tsarin aikin na EFCC ya ƙunshi muradi biyar
A cewar Abdulrasheed Bawa, sabon salon zai bi tsarin yaƙi da cin hanci na ƙasa wato National Anti-Corruption Strategy (NACS) 2017-2021.

Kazalika akwai muradai biyar da zai mayar da hankali a kan su. Su ne:
Ƙara yawan mu'amala da ɗaiɗaikun jama'a a yaƙi da rashawa
Haɓaka tsarukan yaƙi da rashawa ta hanyar daƙile su kafin su faru
Haɓaka bincike ta hanyar tattara bayanan sirri da gurfanarwa a gaban kotu da ƙwato kuɗaɗen sata
Kyautata tabbatar da doka da kuma haɗa gwiwa da mahukunta
Kyautata aiki da ma'aikatu da kuma ma'aikata abokan hulɗar EFCC
Ma'aikatan EFCC

A matsayinta na hukumar yaƙi da laifukan da suka shafi harkokin kuɗi, EFCC ta ce wannan sabon tsarin aiki zai mayar d hankali kacokam wajen aiki tare da aboka hulɗarta na ƙasashen waje.
Manyan abokan hulɗar sun ƙunshi:
Hukumar Federal Bureau of Investigation ta Amurka
Ƙungiyar Tarayyar Turai
Sashen yaƙi da miyagun ƙwayoyi da laifuka na Majalisar Ɗinkin Duniya, 
Gwamnatin Birtaniya
"Mun nuna hakan ƙarara cikin yunƙurinmu na kyautata alaƙa da dukkan hukumomi wanda ya dace da muradi na huɗu na kundin sabon tsarin," a cewar Bawa.


Comments

Popular posts from this blog

Buhari ya fusata da kisar gillar da aka yi wa masu cin kasuwa a garin Goronyo dake gabashin jihar Sokoto.

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yi matukar fusata da kisan gillar da aka yi wa masu cin Kasuwa a Goronyo, Jihar Sokoto inda ya aika wa ƴan bindiga sakon ‘Ta su ta kare’ ranar Litinin. Kakakin fadar shugaban ƙasa, Garba Shehu a wata takarda daga fadar shugaba Buhari ranar Litinin ya bayyana cewa shugaban Buhari ya fusata matuka da kisan da aka yi wa ƴan kasuwa da basu ji ba basu gani ba a kasuwar goronyo. Buhari ya ce wannan karon ƴan bindigan sun kai gwamnati maƙura kuma sun siya da kuɗin su domin sai sun gwammace kiɗa da karatu nan ba da daɗewa ba. ” Ko a yanzu ba su ji da daɗi daga dakarun Najeriya ta sama da kasa ba. Hakan yasa suke bin mutanen da basu ji ba basu gani suna kashe su. Wannan abu ya kai mu makura yanzu kuma lallai su kwana da shirin ta su ta kare. Harin Goronyo A kasuwar Goronyo jihar Sokoto dake ci mako-mako ne ‘yan bindiga suka buda wa mutane wuta inda suka kashe mutum sama da 30 sannan da dama sun ji rauni. Wannan hari ya auku ne kwanaki 12 da wasu ‘ya

Gwamnatin Kaduna ta ce an kashe mutum 343 cikin wata uku a jihar

Daga: Comrade Musa Garba Augie. Gwamnatin Jihar Kaduna ta tabbatar da mutuwar mutum 343 sakamakon ayyukan 'yan fashin daji da sauran tashe-tashen hankali cikin wata uku. Cikin wani rahoto da ya fitar ranar Laraba, Kwamashinan Tsaro da Harkokin Cikin Gida na Kaduna Samuel Aruwan ya bayyana cewa 'yan bindigar da ake zaton 'yan fashin daji ne sun sace mutum 830 a watannin. Rahoton ya duba rikice-rikicen da suka faru ne daga 1 ga watan Yuli zuwa 30 ga Satumban 2021. Sai dai rahoton ya nuna cewa adadin waɗanda aka sace a wata ukun ya ƙaru a kan na watannin Afrilu zuwa Yuni, inda aka sace 774 kuma aka kashe 222. •Na cire ɗana daga makarantar gwamnati saboda 'yan fashi na ƙoƙarin sace shi - El-Rufai •'Yan bindiga sun kai hari Makarantar Sojoji ta NDA •Abin da ya sa El-Rufai ba ya goyon bayan yin sulhu da ƴan bindiga •A gefe guda kuma, Mista Aruwan ya ce jami'an tsaro sun kashe jumillar 'yan fashi 69 a wurare daba-daban na jihar tare da tarwatsa sansanon

Sokoto: 'Ƴan bindiga sun kashe mutum 49 a kasuwar Goronyo'

Tambuwal Rahotanni daga jihar Sokoto a arewa maso yammacin Najeriya na cewa ƴan bidnga sun kashe aƙalla mutum 49 a wata kasuwa a garin Goronyo na jihar. Wasu ganau sun tabbatar wa da BBC labarin inda suka ce lamarin ya faru ne a ranar Lahadi da yamma, yayin da mutanen ke cin babbar kasuwar Goronyon. Mutanen waɗanda suka buƙaci a sakaya sunayensu saboda tsaro sun ce ƴan bindigar sun afka wa kasuwar ne a yayin da ta cika makil da masu hada-hada daga sassan jihar da ma wasu yankunan. "Ƴan fashin sun zo ne da misalin ƙarfe 4.30 zuwa biyar na yamma suka zagaye kasuwar suka buɗe wuta ta kowane ɓangare," in ji ganau ɗin. Majiyarmu ta yi ƙoƙarin jin ta bakin rund8nar ƴan sanda jihar, amma ba mu samu mai magana da yawun ƴan sanda ba a kiran waya da aka yi ta yi masa. Ya ƙara da cewa "Mutane duk suka ruɗe wasu sun kwakkwanta a ƙasa don gudun harbin ya same su, yayin da wasu suka gudu amma masu tsautsayi sun rasa rayukansu." Ganau ɗin sun ce an ƙidaya gawa 49 yayin