Skip to main content

EFCC ta ƙaddamar da sabon salon yaƙi da rashawa a Najeriya



Shugaban EFCC Abdurrashid Bawa

Shugaban EFCC Abdulrasheed Bawa ya ce hukumar za ta fifita daƙile aikata laifuka kafin a aikata su
Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta EFCC a Najeriya ta ce ta ɓullo da wani sabon salon daƙile ayyukan rashawa, inda za ta fi mayar da hankali kan rigakafin daƙile laifin kafin a aikata shi.

A cewar Shugaban EFCC Abdulrasheed Bawa, daga yanzu hukumar za ta fi mayar da hankali wajen haɗa kai da abokan hulɗarta musamman na ƙasashen waje domin yaƙi da ayyukan rashawa.

Da yake magana yayin taron ƙaddamar da sabon tsarin aikin a Abuja, Abdulrasheed Bawa ya ce sabon tsarin na 2021 zuwa 2025 an ciro shi ne daga kundin muradai na EFCC na shekarar 2013 zuwa 2018.
"Sabon salon ya fi fifita rigakafi (hana faruwar laifi) a matsayin hanya mafi sauƙin daƙile rashawa fiye da yin hukunci," a cewarsa kamar yadda mujallar EFCC ta mako-mako ta ruwaito.

Ya ƙara da cewa sabon tsarin zai fifita tattara bayanan sirri da gurfanar da masu laifi a gaban kotu ta hanyar kyautata tsarin aiki.
A watan Yulin 2021 EFCC ta kaddamar da wata manhaja da za ta bai wa 'yan kasa damar ɗaukar hotunan abubuwa ko wuraren da ake aikata laifuka da zummar aika mata da bayanan.

Manyan jami'an Najeriya shida da suka yanke jiki suka faɗi yayin tuhumarsu
An yanke wa ɗan Abdulrasheed Maina hukuncin ɗaurin shekara 24
Muradi biyar
Kundin EFCC.


Sabon kundin tsarin aikin na EFCC ya ƙunshi muradi biyar
A cewar Abdulrasheed Bawa, sabon salon zai bi tsarin yaƙi da cin hanci na ƙasa wato National Anti-Corruption Strategy (NACS) 2017-2021.

Kazalika akwai muradai biyar da zai mayar da hankali a kan su. Su ne:
Ƙara yawan mu'amala da ɗaiɗaikun jama'a a yaƙi da rashawa
Haɓaka tsarukan yaƙi da rashawa ta hanyar daƙile su kafin su faru
Haɓaka bincike ta hanyar tattara bayanan sirri da gurfanarwa a gaban kotu da ƙwato kuɗaɗen sata
Kyautata tabbatar da doka da kuma haɗa gwiwa da mahukunta
Kyautata aiki da ma'aikatu da kuma ma'aikata abokan hulɗar EFCC
Ma'aikatan EFCC

A matsayinta na hukumar yaƙi da laifukan da suka shafi harkokin kuɗi, EFCC ta ce wannan sabon tsarin aiki zai mayar d hankali kacokam wajen aiki tare da aboka hulɗarta na ƙasashen waje.
Manyan abokan hulɗar sun ƙunshi:
Hukumar Federal Bureau of Investigation ta Amurka
Ƙungiyar Tarayyar Turai
Sashen yaƙi da miyagun ƙwayoyi da laifuka na Majalisar Ɗinkin Duniya, 
Gwamnatin Birtaniya
"Mun nuna hakan ƙarara cikin yunƙurinmu na kyautata alaƙa da dukkan hukumomi wanda ya dace da muradi na huɗu na kundin sabon tsarin," a cewar Bawa.


Comments

Popular posts from this blog

Ganduje ya bai wa makaho aiki saboda bajintarsa

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya bai wa Ɗahuru Abdulhamid Idris wanda makaho ne, aikin koyarwa a gwamnatin jihar. Bayanin haka na ƙunshe ne cikin sanarwar da Sakataren Labarai na gwamnatin jihar, Abba Anwar ya fitar a ranar Lahadi. Kafin wannan lokaci, Ɗahuru ya kasance yana aikin koyarwa na sa-kai ba tare da ana biyansa wani albashi ba. Sanarwar ta ce bayan da Kwamishinan Ilimi na Jihar Kano, Muhammadu Sanusi Kiru, ya jagoranci Ɗahuru zuwa gaban Ganduje ne, a nan Ganduje ya bada umarnin a ɗauke shi aiki sannan a tura shi Makarantar Nakasassu da ke Tudun Maliki don ya ci gaba koyarwa. Yayin ganawar tasu, Ganduje ya yaba wa ƙoƙarin Ɗahuru musamman ma ganin yadda bai bari lalurar makanta ta hana shi bada tasa gudunmawa ga cigaban fannin ilimin jihar ba. Bisa wannan dalili ne Gwamna Ganduje ya ce, “Lallai ka taki matakin da ya dace a rayuwarka. Gwamnatin jihar Kano ta ba ka aikin koyarwa. Kuma na umarci Kwamishinan Ilimi da a tura ka zu...

PDP za ta 'Kwace mulki daga hannun APC a zaben 2023 - Inji Atiku Abubakar

Alh. Atiku Abubakar Tsohon mataimakin shugaban kasar Najeriya, Alhaji Atiku Abubakar ya bayyana kwarin gwiwar cewa jam'iyyar PDP, Mai adawa, za ta karbi mulki daga hannun jam'iyyar APC, mai mulki, a zaben shekarar 2023. Atku Abubakar ya bayyana hakan ne yayin da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan ya kada kuri'arsa a dandalin Mahmud Ribadu, Yola, wurin za'ben shugabannin  jam'iyyar PDP na jiha. Ya yi kira ga 'yan siyasa da su mutunta dokokin jam'iyya, na za'be, da Kuma na kundin tsarin mulkin kasar wajen zaben shugabannin jam'iyya, yana mai cewa dimokradiyya na iya 'dorewa ne a cikin yanayi na 'yanci da adalci