Skip to main content

Dokar hana shiga ofis kan korona a Najeriya na tayar da hanakaliMintuna 9 da suka wuceAna yi wa wani allurar rigakafin korona

Dokar hana shiga ofis kan korona a Najeriya na tayar da hanakali
Mintuna 9 da suka wuce
Ana yi wa wani allurar rigakafin korona
Bayan da gwamnatin tarayyar Najeriya ta sanar da cewa daga ranar daya ga watan Disamba duk wani ma'aikacin gwamnatin ba za a bar shi ya shiga ofis ba sai ya nuna shedarsa ta yin rigakafin korona ko kuma shedar ba ya dauke da cutar, ma'aikata da dama na bayyana ra'ayoyin daban-daban.
Sakataren Gwamnatin wanda kuma shi ne shugaban kwamitin da shugaban kasar ya kafa kan yaki da korona Boss Mustapha ne ya sanar da matakin a yayin zaman ƴan kwamitin a Abuja ranar Laraba 13 ga watan Oktoba 2021.

Jaridar Daily Trust ta ambato wani bangare na sanarwar na cewa " daga ranar 1 ga watan Disambar 2021, gwamnatin tarayya za ta bukaci ma'aikatanta su nuna shaidar cewa an yi musu allurar rigakafi ko kuma sakamakon da ke nuna cewa ba su dauke da cutar wanda bai wuce sa'a 72 ba kafin su shiga ofis."

A cewar Sakataren Gwamnatin, kididdigar gwaji ta sama da makonni hudu da suka wuce ta nuna cewa yayin da bazuwar cutar ke raguwa a wasu jihohi, tana karuwa ne a wasu jihohin.

ra'ayoyin wasu daga cikin ma'aikata sa dai mun sakaya sunayensu;
Daga jihar Jigawa wannan cewa ya yi, ''matakin ya yi tsauri, mutane abin da suke fama da shi yanzu shi ne albashi kansa ba ya isar ma'aikata.
"Kuma tuni ai daman matakin da gwamnti ta dauka cewa ma'aikacin da yake daga mataki na 12 zuwa kasa kada ya je aiki, idan dai harkar korona ake magana ai ya isa ya yi magani tun da korona ba ta son cudayya to wannan matakin kadai ya isa, to kuma har a ce sai ka je ka yi wannan allura idan babu ita ba za ka je ofis ba wannan matakin ya yi tsauri gaskiyar magana.

"Kuma zai iya kara sawa mutane hankalinsu ya sake barin gwamnatin gaba daya."
Ana rigakafi
Daga Abuja: "Tun da dai matsala ce wadda ta shafi duniya baki daya ta wannan annoba ta korona ko da yake ita gwamnatin tana so ta yi amfani da wadanda take da iko a kansu, kasancewar wasu jihohi sun yi kokarin su sa a yi amma aka samu tirjiya wannan mataki zai sa a samu mutane da yawa da za su yi rigakafin.

To amma gaskiya gwamnati kamata ya yi ta wayarwa da mutane kai sosai a kan allurar domin har yanzu mutane da dama har ma da ƴan Boko kar ka yi mamaki wadanda suke nuna shakku ko ma zargin cewa rigakafin yana da lahani zai jawo kaza zai jawo kaza. Ko da yake ni na riga na yi nawa.''

Wata ma'aikaciya daga Abuja cewa ta yi, '' Ina ganin ba abu ne da ya zama dole ba, domin hukumar lafiya ta duniya ta riga ta ce allurar rigakafin ba dole ba ce.

"Idan dai har suna son su sa mutane su yi rigakafin ne to bai kamata su tilasta wa mutane su ce lalle sai an yi ba. Mutane da yawa kowa yana da dalilin da ya sa bai yi ba.
"Idan gwamnti ta ce lalle kowa sai ya yi to ta shiga hakkin mutane. Ni dai a yanzu ban yi b kuma ban san abin da zan yi ba idan lokacin d gwamnatin ta yi ya zo.

"Ina fatan lamarin da ba zai kai a ce gwamnati ta tilasta yin allurar ba. Ina fatan za ta sauya shawara kafin lokacin. Kuma ma allurar har guda nawa ake da ita a Najeriya, da za a tilasata wa jama'a?
"Ai allurar ma babu ita wadatacciya a kasar. Gwamnatin ba ta ma shirya wa bin da take magana a kai ba."
WHO: 'Kasashen Afirka na baya a riga-kafin korona'
Abin da ya sa allurar riga-kafin korona miliyan 241 za su yi kwantai
Korona: Italiya ta yi dokar tilasta ma'aikata nuna shedar rigakafi
Wannan kuwa cewa take; "Eh to yana da kyau in dai har zai zama matakin kawo karshen yaduwar cutar koronar ina ganin ya dace tun da har yanzu gwamnati ba ta bayar da umarnin ma'aikata ƴa matakin 12 zuwa kasa su koma aiki ba.

"Ina ga duk yana daga cikin abin da ya sa ba su bari kowa da kowa ya koma aiki ba.
Amma idan har matakin zai zama silar da za ta sa kowa ya koma bakin aiki kuma ya samu kariya daga cutar hakan yana da kyau. Tun da gwamnati ta ce akwai allurar kuma har yanzu ana kan kawowa abu ne da kowa ya kamata ya yi.

"Tun da dai an ga cewa ba wai yana da wata illa ba. Yawancin wadanda suka yi ba wata matsala ce ta samesu da za a ce rigakafin ne ya sa mu in ban da yan kananan matsaloli wadanda ko da ma ba rigakafin ba mutum yana iya samunsu," in ji ta.
Wannan layi ne
Martanin shugaban kungiyar likitoci ta Najeriya
Shugaban kungiyar likitoci ta Najeriyar Dr Uja ya yaba da matakin yana cewa umarnin na gwamnati mataki ne da ya dace wajen yaki da cutar ta korona, inda ya kara da cewa abu da ya shafi bukatar kasa da kuma kulawa.

Ya ce akwai bukatar ƴan Najeriya su kare kansu, yana mai karin bayani da cewa umarnin da shugaban kwamitin da shugaban kasa ya kafa kan yaki da cutar wato Boss Mustapha, kyakkyawan mataki ne na yaki da cutar, wanda kuma ya yi hakan ne ba domin wata muguwar manufa ba, alheri yake nufi da kasar, kamar yadda shugaban kungiyar likitocin ya ce.

Ya ce hakan ya nuna cewa lalle cutar gaskiya ne akwai ta kuma tana nan a tsakanin ƴan Najeriya sosai.
Takunkumi

Zuwa yanzu Najeriya ta samu alkaluman mutane 208,404 da suka kamu da cutar ta korona, da kuma wadanda suka mutu 2,761.
Kasar ta kuma yi wa mutane miliyan biyar daga cikin miliyan 200 rigakafin cutar da magungunan Moderna (MRNA.O) da AstraZeneca (AZN.L) daga wadanda ta samu daga shirin samar da rigakafin na kasashe masu tasowa, COVAX
Haka kuma kasar ta samu allurar rigakafin Johnson & Johnson (JNJ.N) miliyan 1.12 da ta saya daga shirin kungiyar kasashen Afirka kuma tana shirin karbar miliyan 7.7 na Sinopharm (1099.HK) ta hanyar COVAX.

Comments

Popular posts from this blog

Buhari ya fusata da kisar gillar da aka yi wa masu cin kasuwa a garin Goronyo dake gabashin jihar Sokoto.

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yi matukar fusata da kisan gillar da aka yi wa masu cin Kasuwa a Goronyo, Jihar Sokoto inda ya aika wa ƴan bindiga sakon ‘Ta su ta kare’ ranar Litinin. Kakakin fadar shugaban ƙasa, Garba Shehu a wata takarda daga fadar shugaba Buhari ranar Litinin ya bayyana cewa shugaban Buhari ya fusata matuka da kisan da aka yi wa ƴan kasuwa da basu ji ba basu gani ba a kasuwar goronyo. Buhari ya ce wannan karon ƴan bindigan sun kai gwamnati maƙura kuma sun siya da kuɗin su domin sai sun gwammace kiɗa da karatu nan ba da daɗewa ba. ” Ko a yanzu ba su ji da daɗi daga dakarun Najeriya ta sama da kasa ba. Hakan yasa suke bin mutanen da basu ji ba basu gani suna kashe su. Wannan abu ya kai mu makura yanzu kuma lallai su kwana da shirin ta su ta kare. Harin Goronyo A kasuwar Goronyo jihar Sokoto dake ci mako-mako ne ‘yan bindiga suka buda wa mutane wuta inda suka kashe mutum sama da 30 sannan da dama sun ji rauni. Wannan hari ya auku ne kwanaki 12 da wasu ‘ya

Gwamnatin Kaduna ta ce an kashe mutum 343 cikin wata uku a jihar

Daga: Comrade Musa Garba Augie. Gwamnatin Jihar Kaduna ta tabbatar da mutuwar mutum 343 sakamakon ayyukan 'yan fashin daji da sauran tashe-tashen hankali cikin wata uku. Cikin wani rahoto da ya fitar ranar Laraba, Kwamashinan Tsaro da Harkokin Cikin Gida na Kaduna Samuel Aruwan ya bayyana cewa 'yan bindigar da ake zaton 'yan fashin daji ne sun sace mutum 830 a watannin. Rahoton ya duba rikice-rikicen da suka faru ne daga 1 ga watan Yuli zuwa 30 ga Satumban 2021. Sai dai rahoton ya nuna cewa adadin waɗanda aka sace a wata ukun ya ƙaru a kan na watannin Afrilu zuwa Yuni, inda aka sace 774 kuma aka kashe 222. •Na cire ɗana daga makarantar gwamnati saboda 'yan fashi na ƙoƙarin sace shi - El-Rufai •'Yan bindiga sun kai hari Makarantar Sojoji ta NDA •Abin da ya sa El-Rufai ba ya goyon bayan yin sulhu da ƴan bindiga •A gefe guda kuma, Mista Aruwan ya ce jami'an tsaro sun kashe jumillar 'yan fashi 69 a wurare daba-daban na jihar tare da tarwatsa sansanon

Sokoto: 'Ƴan bindiga sun kashe mutum 49 a kasuwar Goronyo'

Tambuwal Rahotanni daga jihar Sokoto a arewa maso yammacin Najeriya na cewa ƴan bidnga sun kashe aƙalla mutum 49 a wata kasuwa a garin Goronyo na jihar. Wasu ganau sun tabbatar wa da BBC labarin inda suka ce lamarin ya faru ne a ranar Lahadi da yamma, yayin da mutanen ke cin babbar kasuwar Goronyon. Mutanen waɗanda suka buƙaci a sakaya sunayensu saboda tsaro sun ce ƴan bindigar sun afka wa kasuwar ne a yayin da ta cika makil da masu hada-hada daga sassan jihar da ma wasu yankunan. "Ƴan fashin sun zo ne da misalin ƙarfe 4.30 zuwa biyar na yamma suka zagaye kasuwar suka buɗe wuta ta kowane ɓangare," in ji ganau ɗin. Majiyarmu ta yi ƙoƙarin jin ta bakin rund8nar ƴan sanda jihar, amma ba mu samu mai magana da yawun ƴan sanda ba a kiran waya da aka yi ta yi masa. Ya ƙara da cewa "Mutane duk suka ruɗe wasu sun kwakkwanta a ƙasa don gudun harbin ya same su, yayin da wasu suka gudu amma masu tsautsayi sun rasa rayukansu." Ganau ɗin sun ce an ƙidaya gawa 49 yayin