Skip to main content

Dokar hana shiga ofis kan korona a Najeriya na tayar da hanakaliMintuna 9 da suka wuceAna yi wa wani allurar rigakafin korona

Dokar hana shiga ofis kan korona a Najeriya na tayar da hanakali
Mintuna 9 da suka wuce
Ana yi wa wani allurar rigakafin korona
Bayan da gwamnatin tarayyar Najeriya ta sanar da cewa daga ranar daya ga watan Disamba duk wani ma'aikacin gwamnatin ba za a bar shi ya shiga ofis ba sai ya nuna shedarsa ta yin rigakafin korona ko kuma shedar ba ya dauke da cutar, ma'aikata da dama na bayyana ra'ayoyin daban-daban.
Sakataren Gwamnatin wanda kuma shi ne shugaban kwamitin da shugaban kasar ya kafa kan yaki da korona Boss Mustapha ne ya sanar da matakin a yayin zaman ƴan kwamitin a Abuja ranar Laraba 13 ga watan Oktoba 2021.

Jaridar Daily Trust ta ambato wani bangare na sanarwar na cewa " daga ranar 1 ga watan Disambar 2021, gwamnatin tarayya za ta bukaci ma'aikatanta su nuna shaidar cewa an yi musu allurar rigakafi ko kuma sakamakon da ke nuna cewa ba su dauke da cutar wanda bai wuce sa'a 72 ba kafin su shiga ofis."

A cewar Sakataren Gwamnatin, kididdigar gwaji ta sama da makonni hudu da suka wuce ta nuna cewa yayin da bazuwar cutar ke raguwa a wasu jihohi, tana karuwa ne a wasu jihohin.

ra'ayoyin wasu daga cikin ma'aikata sa dai mun sakaya sunayensu;
Daga jihar Jigawa wannan cewa ya yi, ''matakin ya yi tsauri, mutane abin da suke fama da shi yanzu shi ne albashi kansa ba ya isar ma'aikata.
"Kuma tuni ai daman matakin da gwamnti ta dauka cewa ma'aikacin da yake daga mataki na 12 zuwa kasa kada ya je aiki, idan dai harkar korona ake magana ai ya isa ya yi magani tun da korona ba ta son cudayya to wannan matakin kadai ya isa, to kuma har a ce sai ka je ka yi wannan allura idan babu ita ba za ka je ofis ba wannan matakin ya yi tsauri gaskiyar magana.

"Kuma zai iya kara sawa mutane hankalinsu ya sake barin gwamnatin gaba daya."
Ana rigakafi
Daga Abuja: "Tun da dai matsala ce wadda ta shafi duniya baki daya ta wannan annoba ta korona ko da yake ita gwamnatin tana so ta yi amfani da wadanda take da iko a kansu, kasancewar wasu jihohi sun yi kokarin su sa a yi amma aka samu tirjiya wannan mataki zai sa a samu mutane da yawa da za su yi rigakafin.

To amma gaskiya gwamnati kamata ya yi ta wayarwa da mutane kai sosai a kan allurar domin har yanzu mutane da dama har ma da ƴan Boko kar ka yi mamaki wadanda suke nuna shakku ko ma zargin cewa rigakafin yana da lahani zai jawo kaza zai jawo kaza. Ko da yake ni na riga na yi nawa.''

Wata ma'aikaciya daga Abuja cewa ta yi, '' Ina ganin ba abu ne da ya zama dole ba, domin hukumar lafiya ta duniya ta riga ta ce allurar rigakafin ba dole ba ce.

"Idan dai har suna son su sa mutane su yi rigakafin ne to bai kamata su tilasta wa mutane su ce lalle sai an yi ba. Mutane da yawa kowa yana da dalilin da ya sa bai yi ba.
"Idan gwamnti ta ce lalle kowa sai ya yi to ta shiga hakkin mutane. Ni dai a yanzu ban yi b kuma ban san abin da zan yi ba idan lokacin d gwamnatin ta yi ya zo.

"Ina fatan lamarin da ba zai kai a ce gwamnati ta tilasta yin allurar ba. Ina fatan za ta sauya shawara kafin lokacin. Kuma ma allurar har guda nawa ake da ita a Najeriya, da za a tilasata wa jama'a?
"Ai allurar ma babu ita wadatacciya a kasar. Gwamnatin ba ta ma shirya wa bin da take magana a kai ba."
WHO: 'Kasashen Afirka na baya a riga-kafin korona'
Abin da ya sa allurar riga-kafin korona miliyan 241 za su yi kwantai
Korona: Italiya ta yi dokar tilasta ma'aikata nuna shedar rigakafi
Wannan kuwa cewa take; "Eh to yana da kyau in dai har zai zama matakin kawo karshen yaduwar cutar koronar ina ganin ya dace tun da har yanzu gwamnati ba ta bayar da umarnin ma'aikata ƴa matakin 12 zuwa kasa su koma aiki ba.

"Ina ga duk yana daga cikin abin da ya sa ba su bari kowa da kowa ya koma aiki ba.
Amma idan har matakin zai zama silar da za ta sa kowa ya koma bakin aiki kuma ya samu kariya daga cutar hakan yana da kyau. Tun da gwamnati ta ce akwai allurar kuma har yanzu ana kan kawowa abu ne da kowa ya kamata ya yi.

"Tun da dai an ga cewa ba wai yana da wata illa ba. Yawancin wadanda suka yi ba wata matsala ce ta samesu da za a ce rigakafin ne ya sa mu in ban da yan kananan matsaloli wadanda ko da ma ba rigakafin ba mutum yana iya samunsu," in ji ta.
Wannan layi ne
Martanin shugaban kungiyar likitoci ta Najeriya
Shugaban kungiyar likitoci ta Najeriyar Dr Uja ya yaba da matakin yana cewa umarnin na gwamnati mataki ne da ya dace wajen yaki da cutar ta korona, inda ya kara da cewa abu da ya shafi bukatar kasa da kuma kulawa.

Ya ce akwai bukatar ƴan Najeriya su kare kansu, yana mai karin bayani da cewa umarnin da shugaban kwamitin da shugaban kasa ya kafa kan yaki da cutar wato Boss Mustapha, kyakkyawan mataki ne na yaki da cutar, wanda kuma ya yi hakan ne ba domin wata muguwar manufa ba, alheri yake nufi da kasar, kamar yadda shugaban kungiyar likitocin ya ce.

Ya ce hakan ya nuna cewa lalle cutar gaskiya ne akwai ta kuma tana nan a tsakanin ƴan Najeriya sosai.
Takunkumi

Zuwa yanzu Najeriya ta samu alkaluman mutane 208,404 da suka kamu da cutar ta korona, da kuma wadanda suka mutu 2,761.
Kasar ta kuma yi wa mutane miliyan biyar daga cikin miliyan 200 rigakafin cutar da magungunan Moderna (MRNA.O) da AstraZeneca (AZN.L) daga wadanda ta samu daga shirin samar da rigakafin na kasashe masu tasowa, COVAX
Haka kuma kasar ta samu allurar rigakafin Johnson & Johnson (JNJ.N) miliyan 1.12 da ta saya daga shirin kungiyar kasashen Afirka kuma tana shirin karbar miliyan 7.7 na Sinopharm (1099.HK) ta hanyar COVAX.

Comments

Popular posts from this blog

Musulmai Sun Yi Martani Ga Gumi Bayan Sukar Da Yayi Akan Maulud

Musulman Najeriya sun mamaye shafin Facebook na Dr. Ahmad Gumi. shahararren mai fafutukar kare hakkin ‘yan fashin daji bayan yayi suka ga maulidi a shafin a daidai lokacin da musulman suke  tunawa da ranar haihuwar Annabi Muhammad SAWA.  A kowace shekara a cikin watan Rabi’ul Awwal, Musulmin duniya suna tunawa da ranar haihuwar Annabi Muhammad ta hanyar karanta Alƙur’ani mai girma, ƙasidun yabo ya Annabi da karanta tarihin rayuwar sa. Shafin Dr. Gumi na Facebook ya samu sharhi sama da 600 har zuwa lokacin nan a tare da cewa suka yayi akan maulidin, amma da yawan su suna rubuta "Happy Maulud,"  duk da sun karanta sukar da yayi.   Karantarwar Dr Gumi tana fuskantar tsaiko da rashin tasiri akan mutane bayan ya karkatar da hankalin sa daga taimakon waɗanda rikicin yan fashin daji ya rutsa da su a arewa maso yammacin Najeriya zuwa neman haƙƙin masu aikata laifin.

PDP za ta 'Kwace mulki daga hannun APC a zaben 2023 - Inji Atiku Abubakar

Alh. Atiku Abubakar Tsohon mataimakin shugaban kasar Najeriya, Alhaji Atiku Abubakar ya bayyana kwarin gwiwar cewa jam'iyyar PDP, Mai adawa, za ta karbi mulki daga hannun jam'iyyar APC, mai mulki, a zaben shekarar 2023. Atku Abubakar ya bayyana hakan ne yayin da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan ya kada kuri'arsa a dandalin Mahmud Ribadu, Yola, wurin za'ben shugabannin  jam'iyyar PDP na jiha. Ya yi kira ga 'yan siyasa da su mutunta dokokin jam'iyya, na za'be, da Kuma na kundin tsarin mulkin kasar wajen zaben shugabannin jam'iyya, yana mai cewa dimokradiyya na iya 'dorewa ne a cikin yanayi na 'yanci da adalci

'Yan bindiga na karbar dafaffen abinci a matsayin kudin fansa a Jihar Kaduna

Gwamnatin Kaduna ta dauki wasu tsauraran matakai domin yaki da 'yan bindiga.  Yanzu haka ‘yan bindiga a Karamar Hukumar Birnin Gwari ta Jihar Kaduna sun bukaci a rika ba su dafaffen abinci a matsayin kudin fansa kafin sakin mutanen da suka yi garkuwa da su. Rahotanni na cewa, ‘yan bindigar sun janye daga kaddamar da hare-hare kan garuruwan jihar tun bayan da gwamnatin ta haramta cin kasuwannin mako-mako a wani bangare na daukar matakin magance matsalar tsaro. Daya daga cikin shugabannin matasan kauyukan Birnin Gwari Babangida Yaro ya shaida wa Jaridar Daily Trsut cewa, tun lokacin da gwamnati ta haramta cin kasuwannin, ‘yan bindigar ke neman a rika ba su dafaffen abinci a duk lokacin da suka sace mutun. Yaro ya kara da cewa, matakin hana sayar da man fetur a yankin, shi ma ya taimaka wajen takaita zirga-zairga. A cewarsa, an samu kwarya-kwaryar zaman lafiya a kauyukan Damari da Kuyello da Kutemashi saboda ‘yan bindigar sun daina kaddamar da farmaki, yayin da suka tare a...