Skip to main content

Buhari ya fusata da kisar gillar da aka yi wa masu cin kasuwa a garin Goronyo dake gabashin jihar Sokoto.


Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yi matukar fusata da kisan gillar da aka yi wa masu cin Kasuwa a Goronyo, Jihar Sokoto inda ya aika wa ƴan bindiga sakon ‘Ta su ta kare’ ranar Litinin.

Kakakin fadar shugaban ƙasa, Garba Shehu a wata takarda daga fadar shugaba Buhari ranar Litinin ya bayyana cewa shugaban Buhari ya fusata matuka da kisan da aka yi wa ƴan kasuwa da basu ji ba basu gani ba a kasuwar goronyo.

Buhari ya ce wannan karon ƴan bindigan sun kai gwamnati maƙura kuma sun siya da kuɗin su domin sai sun gwammace kiɗa da karatu nan ba da daɗewa ba.

” Ko a yanzu ba su ji da daɗi daga dakarun Najeriya ta sama da kasa ba. Hakan yasa suke bin mutanen da basu ji ba basu gani suna kashe su. Wannan abu ya kai mu makura yanzu kuma lallai su kwana da shirin ta su ta kare.

Harin Goronyo

A kasuwar Goronyo jihar Sokoto dake ci mako-mako ne ‘yan bindiga suka buda wa mutane wuta inda suka kashe mutum sama da 30 sannan da dama sun ji rauni.

Wannan hari ya auku ne kwanaki 12 da wasu ‘yan bindiga suka kashe mutane a kasuwar Unguwar Lalle dake karamar hukumar Sabon Birni.

A jihar Sokoto kananan hukumomin Goronyo, Isa, Sabon Birni da Raba wurare ne da ‘yan bindiga suka addaba da hare-hare.

Wani dake kare rajin dan Adam a jihar Sokoto Basharu Guyawa ya ce maharan d suka kau su akalla 200 sai da suka zagaye kasuwar sannan suka bude wa mutane wuta ta ko ina.

Ya ce ‘yan bindigan sun dauki awowi suna barin wuta a kasuwar, ba a dai iya fayyace ko mutum naya suka sheka lahira a dalilin wannan hari ba, saidai an kiyasta cewa an ga gawarwaki sama da 30 wanda aka kashe nan take.

Wani mazaunin garin kuma tsohon ma’aikacin gwamnati Bashir Adamu ya ce ba za su taba manta wa da wannan rana ta Lahadi ba.

Ya ce maharan sun kashe mutum sama da 30 sannan mutum 20 sun ji rauni.

A ziyarar jaje da babban ahfsan sojojin Najeriya Faruk Yahaya ya kai wa gwamnan Sokoto ranar Litinin, ya tabbatar wa gwamna AMinu Tambuwal cewa za a ci gaba da suburbudar yan bindigan a lo’ina suka a fadin kasar nan.

” Wannan wannan mummunar hari ne da ba shi misaltuwa da komai. Ina kira ga rundunar soji da ta turo karin jami’ai jihar domin gamawa da ‘yan bindigan da suka addabi mutanen yankin jihar.

Rahoto: Salisu Idris Waziri

Comments

Popular posts from this blog

Gwamnatin Kaduna ta ce an kashe mutum 343 cikin wata uku a jihar

Daga: Comrade Musa Garba Augie. Gwamnatin Jihar Kaduna ta tabbatar da mutuwar mutum 343 sakamakon ayyukan 'yan fashin daji da sauran tashe-tashen hankali cikin wata uku. Cikin wani rahoto da ya fitar ranar Laraba, Kwamashinan Tsaro da Harkokin Cikin Gida na Kaduna Samuel Aruwan ya bayyana cewa 'yan bindigar da ake zaton 'yan fashin daji ne sun sace mutum 830 a watannin. Rahoton ya duba rikice-rikicen da suka faru ne daga 1 ga watan Yuli zuwa 30 ga Satumban 2021. Sai dai rahoton ya nuna cewa adadin waɗanda aka sace a wata ukun ya ƙaru a kan na watannin Afrilu zuwa Yuni, inda aka sace 774 kuma aka kashe 222. •Na cire ɗana daga makarantar gwamnati saboda 'yan fashi na ƙoƙarin sace shi - El-Rufai •'Yan bindiga sun kai hari Makarantar Sojoji ta NDA •Abin da ya sa El-Rufai ba ya goyon bayan yin sulhu da ƴan bindiga •A gefe guda kuma, Mista Aruwan ya ce jami'an tsaro sun kashe jumillar 'yan fashi 69 a wurare daba-daban na jihar tare da tarwatsa sansanon

Sokoto: 'Ƴan bindiga sun kashe mutum 49 a kasuwar Goronyo'

Tambuwal Rahotanni daga jihar Sokoto a arewa maso yammacin Najeriya na cewa ƴan bidnga sun kashe aƙalla mutum 49 a wata kasuwa a garin Goronyo na jihar. Wasu ganau sun tabbatar wa da BBC labarin inda suka ce lamarin ya faru ne a ranar Lahadi da yamma, yayin da mutanen ke cin babbar kasuwar Goronyon. Mutanen waɗanda suka buƙaci a sakaya sunayensu saboda tsaro sun ce ƴan bindigar sun afka wa kasuwar ne a yayin da ta cika makil da masu hada-hada daga sassan jihar da ma wasu yankunan. "Ƴan fashin sun zo ne da misalin ƙarfe 4.30 zuwa biyar na yamma suka zagaye kasuwar suka buɗe wuta ta kowane ɓangare," in ji ganau ɗin. Majiyarmu ta yi ƙoƙarin jin ta bakin rund8nar ƴan sanda jihar, amma ba mu samu mai magana da yawun ƴan sanda ba a kiran waya da aka yi ta yi masa. Ya ƙara da cewa "Mutane duk suka ruɗe wasu sun kwakkwanta a ƙasa don gudun harbin ya same su, yayin da wasu suka gudu amma masu tsautsayi sun rasa rayukansu." Ganau ɗin sun ce an ƙidaya gawa 49 yayin