Skip to main content

"Annabi Ne Ya Fara Maulidi, Saboda Haka Ba Bidi'a Ba Ne" ~Sheikh Halliru Mataya

FILIN FAHIMTA FUSKA:


Sheikh Maraya ya ce annabi ne ya fara yin nuni ga murnar ranar haihuwarsa Sheikh Halliru Maraya, malamin addini a Kaduna ya ce Annabi Muhammad SAW ne ya fara yin nuni ga murnar ranar haihuwarsa da ake kira Maulidi.

"An tambayi Annabi Muhammad SAW dangane da azumin Litinin da ya ke yi.

Sai annabin ya ce ranar ne aka haife ni", in ji Sheikh Halliru.

Malamin ya kara da cewa kamata ya yi Musulmi su girmama watan na Maulidi kasancewar a watan ne Allah ubangiji ya bai wa duniya kyautar da babu irinta ga. duniya wato haihuwar Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi.

Abubuwan da ya kamata a yi lokacin Maulidi: Malamin ya lissafa wasu. abubuwan da ya kamata a yi a lokacin Maulidi amma wadanda ba
su saba da shari'a ba.

Sai dai malamin ya ce bai kamata a yi duk abin da shari'a ba ta amince da shi ba kamar cakuɗuwar maza da mata, ihuce-ihuce, shaye-shaye da dai sauransu.

Rabi'ul Awwal, wata ne na kalandar musulunci da wani ɓangaren musulmin duniya ke bikin. zagayowar ranar da aka haifi manzon Allah, Annabi Muhammad S.A.W.

Musulmai da dama sun yi amannar cewa a watan Rabi'ul Awwal, aka haifi Annabi Muhammadu (SAW).

Sai dai ba dukkanin Musulmi ne ke bikin haihuwar Ma'aiki SAW, saboda sabanin fahimta.

Akwai wani ɓangare na malamai da ke nuna rashin dacewar gudanar da bikin maulidi.

Comments

Popular posts from this blog

Musulmai Sun Yi Martani Ga Gumi Bayan Sukar Da Yayi Akan Maulud

Musulman Najeriya sun mamaye shafin Facebook na Dr. Ahmad Gumi. shahararren mai fafutukar kare hakkin ‘yan fashin daji bayan yayi suka ga maulidi a shafin a daidai lokacin da musulman suke  tunawa da ranar haihuwar Annabi Muhammad SAWA.  A kowace shekara a cikin watan Rabi’ul Awwal, Musulmin duniya suna tunawa da ranar haihuwar Annabi Muhammad ta hanyar karanta Alƙur’ani mai girma, ƙasidun yabo ya Annabi da karanta tarihin rayuwar sa. Shafin Dr. Gumi na Facebook ya samu sharhi sama da 600 har zuwa lokacin nan a tare da cewa suka yayi akan maulidin, amma da yawan su suna rubuta "Happy Maulud,"  duk da sun karanta sukar da yayi.   Karantarwar Dr Gumi tana fuskantar tsaiko da rashin tasiri akan mutane bayan ya karkatar da hankalin sa daga taimakon waɗanda rikicin yan fashin daji ya rutsa da su a arewa maso yammacin Najeriya zuwa neman haƙƙin masu aikata laifin.

PDP za ta 'Kwace mulki daga hannun APC a zaben 2023 - Inji Atiku Abubakar

Alh. Atiku Abubakar Tsohon mataimakin shugaban kasar Najeriya, Alhaji Atiku Abubakar ya bayyana kwarin gwiwar cewa jam'iyyar PDP, Mai adawa, za ta karbi mulki daga hannun jam'iyyar APC, mai mulki, a zaben shekarar 2023. Atku Abubakar ya bayyana hakan ne yayin da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan ya kada kuri'arsa a dandalin Mahmud Ribadu, Yola, wurin za'ben shugabannin  jam'iyyar PDP na jiha. Ya yi kira ga 'yan siyasa da su mutunta dokokin jam'iyya, na za'be, da Kuma na kundin tsarin mulkin kasar wajen zaben shugabannin jam'iyya, yana mai cewa dimokradiyya na iya 'dorewa ne a cikin yanayi na 'yanci da adalci

'Yan bindiga na karbar dafaffen abinci a matsayin kudin fansa a Jihar Kaduna

Gwamnatin Kaduna ta dauki wasu tsauraran matakai domin yaki da 'yan bindiga.  Yanzu haka ‘yan bindiga a Karamar Hukumar Birnin Gwari ta Jihar Kaduna sun bukaci a rika ba su dafaffen abinci a matsayin kudin fansa kafin sakin mutanen da suka yi garkuwa da su. Rahotanni na cewa, ‘yan bindigar sun janye daga kaddamar da hare-hare kan garuruwan jihar tun bayan da gwamnatin ta haramta cin kasuwannin mako-mako a wani bangare na daukar matakin magance matsalar tsaro. Daya daga cikin shugabannin matasan kauyukan Birnin Gwari Babangida Yaro ya shaida wa Jaridar Daily Trsut cewa, tun lokacin da gwamnati ta haramta cin kasuwannin, ‘yan bindigar ke neman a rika ba su dafaffen abinci a duk lokacin da suka sace mutun. Yaro ya kara da cewa, matakin hana sayar da man fetur a yankin, shi ma ya taimaka wajen takaita zirga-zairga. A cewarsa, an samu kwarya-kwaryar zaman lafiya a kauyukan Damari da Kuyello da Kutemashi saboda ‘yan bindigar sun daina kaddamar da farmaki, yayin da suka tare a...